< Yoshuwa 19 >

1 Ƙuri’a ta biyu ta fāɗa a kan kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu. Ƙasarsu ta gādo tana cikin yankin Yahuda.
둘째로 시므온 곧 시므온 자손의 지파를 위하여 그 가족대로 제비를 뽑았으니 그 기업은 유다 자손의 기업 중에서라
2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda. Beyersheba (ko Sheba), Molada,
그 얻은 기업은 브엘세바 곧 세바와, 몰라다와,
3 Hazar Shuwal, Bilha, Ezem,
하살 수알과, 발라와, 에셈과,
4 Eltolad, Betul, Horma,
엘돌랏과, 브둘과, 호르마와,
5 Ziklag, Bet-Markabot, Hazar-Susa,
시글락과, 벧 말가봇과, 하살수사와,
6 Bet-Lebayot da Sharuhen, garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu.
벧 르바옷과, 사루헨이니 십 삼 성읍이요 또 그 촌락이며
7 Akwai kuma Ayin, Rimmon, Eter da Ashan, garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu,
또 아인과 림몬과, 에델과 아산이니 네 성읍이요 또 그 촌락이며
8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da garuruwan nan har zuwa Rama na Negeb (wato, Ba’alat-Beyer). Wannan shi ne gādon kabilar Simeyon bisa ga iyalansu.
또 남방 라마 곧 바알랏 브엘까지 이 성들을 둘러 있는 모든 촌락이니 이는 시므온 자손의 지파가 그 가족대로 얻은 기업이라
9 Daga cikin gādon mutanen Yahuda ne aka fitar da gādon kabilar Simeyon, bisa ga iyalansu, domin rabon da kabilar Yahuda suka samu ya fi ƙarfin abin da suke bukata. Saboda haka kabilar gādon Simeyon yana cikin harabar Yahuda.
시므온 자손의 이 기업은 유다 자손의 기업 중에서 취하였으니 이는 유다 자손의 분깃이 자기들에게 너무 많으므로 시므온 자손이 자기의 기업을 그들의 기업 중에서 얻음이었더라
10 Ƙuri’a ta uku ta fāɗa a kan Zebulun bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kai har Sarid.
세째로 스불론 자손을 위하여 그 가족대로 제비를 뽑았으니 그 기업의 경계는 사릿에 미치고
11 Ta nufi yamma zuwa Marala, ta taɓa Dabbeshet, ta wuce zuwa rafin da yake kusa da Yokneyam.
서편으로 올라가서 마랄라에 이르러 답베셋에 미치고 욕느암 앞 시내에 미치며
12 Daga Sarid, ta juya gabas zuwa harabar Kislot Tabor, ta kuma wuce zuwa Daberat har zuwa Yafiya.
사릿에서부터 동편으로 돌아 해 뜨는 편을 향하고 기슬롯 다볼의 경계에 이르고 다브랏으로 나가서 야비아로 올라가고
13 Sa’an nan ta ci gaba, ta yi gabas zuwa Gat-Hefer da Et Kazin; ta ɓulla a Rimmon, ta juya zuwa Neya.
또 거기서부터 동편으로 가드 헤벨을 지나 엣 가신에 이르고 네아까지 연한 림몬으로 나아가서
14 A can ne iyakar ta kewaya zuwa Hannaton, sa’an nan ta ƙarasa a Kwarin Ifta El.
북으로 돌아 한나돈에 이르고 입다엘 골짜기에 이르러 끝이 되며
15 Zebulun ta ƙunshi garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu. Garuruwan sun haɗa da Kattat, Nahalal, Shimron, Idala da Betlehem.
또 갓닷과, 나할랄과, 시므론과, 이달라와, 베들레헴이니 모두 십 이성읍이요 또 그 촌락이라
16 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Zebulun ta samu, bisa ga iyalansu.
스불론 자손이 그 가족대로 얻은 기업은 이 성읍들과 그 촌락이었더라
17 Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.
네째로 잇사갈 곧 잇사갈 자손을 위하여 그 가족대로 제비를 뽑았으니
18 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,
그 지경 안은 이스르엘과, 그술롯과, 수넴과,
19 Hafarayim, Anaharat,
하바라임과, 시온과, 아나하랏과,
20 Rabbat, Kishiyon, Ebez,
랍빗과, 기시온과, 에베스와,
21 Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.
레멧과, 언간님과, 엔핫다와, 벧 바세스며,
22 Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
그 경계는 다볼과 사하수마와 벧 세메스에 미치고 그 끝은 요단이니 모두 십 육 성읍이요 또 그 촌락이라
23 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.
잇사갈 자손 지파가 그 가족대로 얻은 기업은 이 성읍들과 그 촌락이었더라
24 Ƙuri’a ta biyar ta fāɗa a kan kabilar Asher, bisa ga iyalansu.
다섯째로 아셀 자손의 지파를 위하여 그 가족대로 제비를 뽑았으니
25 Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
그 지경 안은 헬갓과, 할리와, 베덴과, 악삽과,
26 Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
알람멜렉과, 아맛과, 미살이며 그 경계의 서편은 갈멜에 미치며 시홀 림낫에 미치고
27 Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
꺾여 해 돋는 편을 향하여 벧 다곤에 이르며 스불론에 달하고 북편으로 입다 엘 골짜기에 미쳐서 벧에멕과 느이엘에 이르고 가불 좌편으로 나가서
28 ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
에브론과, 르홉과, 함몬과, 가나를 지나 큰 시돈까지 이르고
29 Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
돌아서 라마와 견고한 성읍 두로에 이르고 돌아서 호사에 이르고 악십 지방 곁 바다가 끝이 되며
30 Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
또 움마와, 아벡과, 르홉이니 모두 이십 이 성읍과 그 촌락이라
31 Garuruwan nan da ƙauyukansu su ne gādon da kabilar Asher ta samu bisa ga iyalansu.
아셀 자손의 지파가 그 가족대로 얻은 기업은 이 성읍들과 그 촌락이었더라
32 Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.
여섯째로 납달리 자손을 위하여 납달리 자손의 가족대로 제비를 뽑았으니
33 Iyakarsu ta kama daga Helef, daga babban itacen Mamre nan da yake a Za’anannim, ta wuce Adami Nekeb da Yabneyel zuwa Lakkum, ta kuma ƙarasa a Urdun.
그 경계는 헬렙과 사아난님의 상수리나무에서부터 아다미 네겝과 얍느엘을 지나 락굼까지요 그 끝은 요단이며
34 Iyakar kuma ta juya yamma ta cikin Aznot-Tabo ta ɓulla a Hukkok. Ta taɓa Zebulun a kudu, Asher a yamma, da kuma Urdun a gabas.
서편으로 돌아 아스놋 다볼에 이르고 그 곳에서부터 나가 훅곡에 이르러는 남은 스불론에 접하였고 서는 아셀에 접하였으며 해 돋는 편은 유다에 달한 요단이며
35 Biranen da suke da katanga su ne Ziddim, Zer, Hammat, Rakkat, Kinneret,
그 견고한 성읍들은 싯딤과, 세르와, 함맛과, 락갓과, 긴네렛과,
36 Adama, Rama, Hazor,
아다마와, 라마와, 하솔과,
37 Kedesh, Edireyi, En Hazor,
게데스와, 에드레이와, 엔 하솔과,
38 Yiron, Migdal El, Horem, Bet-Anat da Bet-Shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu.
이론과, 믹다렐과, 호렘과, 벧 아낫과, 벧 세메스니 모두 십 구 성읍이요 또 그 촌락이라
39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.
납달리 자손의 지파가 그 가족대로 얻은 기업은 이 성읍들과 그 촌락이었더라
40 Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
일곱째로 단 자손의 지파를 위하여 그 가족대로 제비를 뽑았으니
41 Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
그 기업의 지경은 소라와, 에스다올과, 이르세메스와,
42 Shalim, Aiyalon, Itla,
사알랍빈과, 아얄론과, 이들라와,
43 Elon, Timna, Ekron,
엘론과, 딤나와, 에그론과,
44 Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
엘드게와, 깁브돈과, 바알랏과,
45 Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
여훗과, 브네브락과, 가드 림몬과,
46 Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
메얄곤과, 락곤과, 욥바 맞은편 경계까지라
47 (Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
그런데 단 자손의 지경이 더욱 확장되었으니 이는 단 자손이 올라가서 레센을 쳐서 취하여 칼날로 치고 그것을 얻어 거기 거하였음이라 그 조상 단의 이름을 따라서 레센을 단이라 하였더라
48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
단 자손의 지파가 그 가족대로 얻은 기업은 이 성읍들과 그 촌락이었더라
49 Sa’ad da aka gama raba gādon ƙasar bisa ga ƙuri’a. Sai Isra’ilawa suka ba Yoshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikinsu,
이스라엘 자손이 그 경계를 따라서 기업의 땅 나누기를 마치고 자기들 중에서 눈의 아들 여호수아에게 기업을 주었으되
50 yadda Ubangiji ya umarta, suka ba shi garin da ya ce a ba shi, Timnat Serad a ƙasar tudu ta Efraim. Ya kuma gina garin ya zauna a can.
곧 여호와의 명령대로 여호수아의 구한 성읍 에브라임 산지 딤낫 세라를 주매 여호수아가 그 성읍을 중건하고 거기 거하였었더라
51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin kabilan iyalan Isra’ila suka rarraba ta hanyar jefa ƙuri’a a Shilo a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada. Da haka suka yi suka gama rarraba ƙasar.
제사장 엘르아살과 눈의 아들 여호수아와 이스라엘 자손 지파의 족장들이 실로에서 회막문 여호와 앞에서 제비 뽑아 나눈 기업이 이러하니라 이에 땅 나누는 일이 마쳤더라

< Yoshuwa 19 >