< Yoshuwa 16 >

1 Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
The lot came out for the descendants of Joseph from the Jordan at Jericho, at the waters of Jericho on the east, even the wilderness, going up from Jericho through the hill country to Bethel.
2 Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
It went out from Bethel to Luz, and passed along to the border of the Archites at Ataroth;
3 ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
and it went down westward to the border of the Japhletites, to the border of Lower Beth Horon, even to Gezer; and ended at the sea.
4 Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
The descendants of Joseph, Manasseh and Ephraim, took their inheritance.
5 Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
This was the border of the descendants of Ephraim according to their families. The border of their inheritance eastward was Ataroth Addar, to Upper Beth Horon.
6 ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
The border went out westward at Michmethath on the north of Termah. The border turned about eastward to Taanath Shiloh, and passed along it on the east of Janoah.
7 Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
It went down from Janoah to Ataroth, to Naaratah, reached to Jericho, and went out at the Jordan.
8 Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
From Tappuah the border went along westward to Wadi Kanah; and ended at the sea. This is the inheritance of the tribe of the descendants of Ephraim according to their families;
9 Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
together with the cities which were set apart for the descendants of Ephraim in the midst of the inheritance of the descendants of Manasseh, all the cities with their villages.
10 Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.
They did not drive out the Canaanites who lived in Gezer; but the Canaanites dwell in the midst of Ephraim to this day, and have become servants to do forced labor.

< Yoshuwa 16 >