< Yunana 2 >

1 Daga ciki cikin kifi, Yunana ya yi addu’a ga Ubangiji Allahnsa.
Then Jonah prayed to Yahweh, his God, out of the fish’s belly.
2 Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol h7585)
He said, “I called because of my affliction to Yahweh. He answered me. Out of the belly of Sheol I cried. You heard my voice. (Sheol h7585)
3 Cikin tashin hankali, ka jefa ni cikin zurfafa, a tsakiyar teku, ka kuma jujjuya ni a cikin ruwa; dukan raƙuman ruwanka da ambaliyarka sun bi ta kaina.
For you threw me into the depths, in the heart of the seas. The flood was all around me. All your waves and your billows passed over me.
4 Sai na ce, ‘An kore ni daga fuskarka; duk da haka zan sāke duba wajen haikalinka mai tsarki.’
I said, ‘I have been banished from your sight; yet I will look again toward your holy temple.’
5 Ruwayen da suke kewaye da ni sun yi mini barazana, zurfi kuma ya kewaye ni, ciyayin ruwa suna nannaɗe kewaye da ni.
The waters surrounded me, even to the soul. The deep was around me. The weeds were wrapped around my head.
6 Na nutsa har ƙarƙashin tuddai; a ƙarƙashin duniya, ka rufe ni har abada. Amma ka dawo da raina daga rami, Ya Ubangiji Allahna.
I went down to the bottoms of the mountains. The earth barred me in forever; yet you have brought my life up from the pit, Yahweh my God.
7 “Sa’ad da na ji raina yana rabuwa da ni, na tuna da kai ya Ubangiji, addu’ata kuma ta kai gare ka, a haikalinka mai tsarki.
“When my soul fainted within me, I remembered Yahweh. My prayer came in to you, into your holy temple.
8 “Waɗanda suka maƙale wa gumaka marasa amfani, sukan ƙyale alherin da zai kasance nasu.
Those who regard vain idols forsake their own mercy.
9 Amma ni, da waƙar godiya, zan miƙa tawa hadaya gare ka. Abin da na yi alkawari, shi ne zan yi. Ceto yakan zo ne kawai daga wurin Ubangiji.”
But I will sacrifice to you with the voice of thanksgiving. I will pay that which I have vowed. Salvation belongs to Yahweh.”
10 Sai Ubangiji ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunana a gaɓan teku.
Then Yahweh spoke to the fish, and it vomited out Jonah on the dry land.

< Yunana 2 >