< Yohanna 9 >

1 Da Yesu yana tafiya, sai ya ga wani mutum wanda aka haifa makaho.
And when he went on his way, he saw a man blind from birth.
2 Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, wane ne ya yi zunubi, mutumin ne, ko iyayensa, da ya sa aka haife shi makaho?”
And his disciples put a question to him, saying, Master, was it because of this man's sin, or the sin of his father and mother, that he has been blind from birth?
3 Sai Yesu ya ce, “Ba don mutumin ko iyayensa sun yi zunubi ne ba, sai dai don a bayyana aikin Allah ne a rayuwarsa.
Jesus said in answer, It was not because of his sin, or because of his father's or mother's; it was so that the works of God might be seen openly in him.
4 Muddin da sauran rana, dole mu yi aikin wanda ya aiko ni. Dare yana zuwa, sa’ad da ba wanda zai iya yin aiki.
While it is day we have to do the works of him who sent me: the night comes when no work may be done.
5 Yayinda ina a cikin duniya, ni ne hasken duniya.”
As long as I am in the world, I am the light of the world.
6 Bayan ya faɗi haka, sai ya tofa miyau a ƙasa, ya kwaɓa laka da miyau ɗin, ya kuma shafa a idanun mutumin.
Having said these words, he put earth, mixed with water from his mouth, on the man's eyes,
7 Ya ce masa, “Je ka, ka wanke a Tafkin Silowam” (kalman nan tana nufin “Aikakke”). Saboda haka mutumin ya tafi ya wanke, ya kuma dawo gida yana gani.
And said to him, Go and make yourself clean in the bath of Siloam (the sense of the name is, Sent). So he went away and, after washing, came back able to see.
8 Maƙwabta da waɗanda suka saba ganinsa dā yana bara, suka ce, “Kai, ba wannan mutum ne ya saba zama yana bara ba?”
Then the neighbours and others who had seen him before in the street, with his hand out for money, said, Is not this the man who got money from people?
9 Waɗansu suka ce shi mana. Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ya dai yi kama da shi.” Amma shi ɗin ya ce, “Ƙwarai kuwa ni ne.”
Some said, It is he: others said, No, but he is like him. He said, I am he.
10 Sai suka ce, “To, yaya aka yi idanunka suka buɗe?”
So they said to him, How then were your eyes made open?
11 Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
His answer was: The man who is named Jesus put earth mixed with water on my eyes, and said to me, Go and make yourself clean in Siloam: so I went away and, after washing, am now able to see.
12 Suka tambaye shi suka ce, “Ina mutumin yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”
And they said to him, Where is he? His answer was: I have no knowledge.
13 Sai suka kawo mutumin da dā yake makaho wurin Farisiyawa.
They took him before the Pharisees — this man who had been blind.
14 To, a ranar da Yesu ya kwaɓa laka ya buɗe idanun mutumin ranar Asabbaci ce.
Now the day on which the earth was mixed by Jesus and the man's eyes were made open was the Sabbath.
15 Saboda haka Farisiyawa suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Mutumin ya amsa, “Ya shafa laka a idanuna, sai na wanke, ina kuwa gani.”
So the Pharisees put more questions to him about how his eyes had been made open. And he said to them, He put earth on my eyes, and I had a wash and am able to see.
16 Sai waɗansu daga cikin Farisiyawa suka ce, “Mutumin nan ba daga Allah yake ba, don ba ya kiyaye ranar Asabbaci.” Amma waɗansu suka yi tambaya suka ce, “Yaya mutum mai zunubi zai yi irin abubuwan banmamaki haka?” Sai ra’ayinsu ya sha bamban.
Then some of the Pharisees said, That man has not come from God, for he does not keep the Sabbath. Others said, How is it possible for a sinner to do such signs? So there was a division among them.
17 A ƙarshe suka sāke koma ga makahon suka ce, “Kai fa, me ka gani game da shi? Idanunka ne fa ya buɗe.” Sai mutumin ya ce, “Tab, ai, shi annabi ne.”
Again they said to the blind man, What have you to say about him for opening your eyes? And he said, He is a prophet.
18 Yahudawa dai ba su yarda cewa dā shi makaho ne ya kuma sami ganin gari ba, sai da suka kira iyayen mutumin.
Now the Jews had no belief in the statement that he had been blind and was now able to see, till they sent for the father and mother of the man whose eyes had been made open,
19 Suka tambaye su, “Wannan ɗanku ne? Shi ne wanda kuka ce an haife shi makaho? To, ta yaya yake gani yanzu?”
And put the question to them, saying, Is this your son, of whom you say that he was blind at birth? how is it then that he is now able to see?
20 Iyayen suka amsa suka ce, “Mun dai san shi ɗanmu ne, mun kuma san cewa an haife shi makaho.
In answer his father and mother said, We are certain that this is our son and that he was blind at birth:
21 Sai dai yadda yake gani yanzu, ko kuma wa ya buɗe idanunsa, ba mu sani ba. Ku tambaye shi. Ai, shi ba yaro ba ne, zai faɗa da bakinsa.”
But how it is he is now able to see, or who made his eyes open, we are not able to say: put the question to him; he is old enough to give an answer for himself.
22 Iyayensa sun faɗa haka ne saboda suna tsoron Yahudawa, gama Yahudawa sun riga sun yanke shawara cewa duk wanda ya yarda cewa Yesu shi ne Kiristi, za a kore shi daga majami’a.
They said this because of their fear of the Jews: for the Jews had come to an agreement that if any man said that Jesus was the Christ he would be put out of the Synagogue.
23 Shi ya sa iyayensa suka ce, “Ai, shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
That was the reason why they said, He is old enough; put the question to him.
24 Sai suka sāke kiran mutumin nan da yake makaho a dā, suka ce masa, “Ka ɗaukaka Allah, mu kam, mun san mutumin nan mai zunubi ne.”
So they sent a second time for the man who had been blind and they said to him, Give glory to God: it is clear to us that this man is a sinner.
25 Sai ya amsa ya ce, “Ko shi mai zunubi ne ko babu, ni dai ban sani ba. Abu ɗaya fa na sani, dā ni makaho ne, amma yanzu ina gani!”
He said in answer, I have no knowledge if he is a sinner or not, but one thing I am certain about; I was blind, and now I see.
26 Sai suka tambaye suka ce, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe idanunka?”
Then they said to him, What did he do to you? how did he give you the use of your eyes?
27 Ya amsa ya ce, “Na riga na gaya muku ba ku kuwa saurara ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?”
His answer was: I have said it before, but your ears were shut: why would you have me say it again? is it your desire to become his disciples?
28 Sai suka hau shi da zagi suna cewa, “Kai ne dai almajirin mutumin! Mu almajiran Musa ne!
And they were angry with him and said, You are his disciple, but we are disciples of Moses.
29 Mun dai san cewa Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum ba mu san inda ya fito ba.”
We are certain that God gave his word to Moses: but as for this man, we have no knowledge where he comes from.
30 Sai mutumin ya ce, “Cabɗi, yau ga abin mamaki! Ba ku san inda ya fito ba, ga shi kuwa ya buɗe idanuna.
The man said in answer, Why, here is a strange thing! You have no knowledge where he comes from though he gave me the use of my eyes.
31 Mun san cewa Allah ba ya sauraron masu zunubi. Yakan saurari mai tsoronsa mai aikata nufinsa.
We have knowledge that God does not give ear to sinners, but if any man is a worshipper of God and does his pleasure, to him God's ears are open.
32 Ba wanda ya taɓa ji cewa an buɗe idanun wanda aka haifa makaho. (aiōn g165)
In all the years nobody has ever before seen the eyes of a man blind from birth made open. (aiōn g165)
33 Da mutumin nan ba daga Allah ba ne, da ba abin da zai iya yi.”
If this man did not come from God he would be unable to do anything.
34 Sai suka amsa suka ce, “Kai da aka haifa cike da zunubi; za ka yi karambanin koyarwar da mu!” Sai suka kore shi.
Their answer was: You came to birth through sin; do you make yourself our teacher? And they put him out of the Synagogue.
35 Yesu ya ji labari cewa sun kore shi, da ya same shi kuwa, sai ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum?”
It came to the ears of Jesus that they had put him out, and meeting him he said, Have you faith in the Son of man?
36 Sai mutumin ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, wane ne shi? Gaya mini, don in gaskata da shi.”
He said in answer, And who is he, Lord? Say, so that I may have faith in him.
37 Yesu ya ce, “Yanzu ka gan shi; tabbatacce ma, shi ne yake magana da kai.”
Jesus said to him, You have seen him; it is he who is talking to you.
38 Sai mutumin ya ce, “Ubangiji, na gaskata,” ya kuma yi masa sujada.
And he said, Lord, I have faith. And he gave him worship.
39 Yesu ya ce, “Saboda shari’a ce na zo duniya nan, saboda makafi su sami ganin gari, waɗanda suke gani kuma su makance.”
And Jesus said, I came into this world to be a judge, so that those who do not see may see, and those who see may become blind.
40 Da Farisiyawan da suke tare da shi suka ji ya faɗi haka sai suka yi tambaya suka ce, “Mene? Mu ma makafi ne?”
These words came to the ears of the Pharisees who were with him and they said to him, Are we, then, blind?
41 Yesu ya ce, “Ai, da ku makafi ne ma, da ba ku da zunubi, amma da yake kun ce, kuna gani, zunubanku suna nan daram.
Jesus said to them, If you were blind you would have no sin: but now that you say, We see; your sin is there still.

< Yohanna 9 >