< Yohanna 7 >

1 Bayan wannan, sai Yesu ya yi ta zagawa a cikin Galili, da ganga bai yarda yă je Yahudiya ba domin Yahudawa a can suna nema su kashe shi.
After this, Jesus went from place to place in Galilee. He did not go about in Judaea, because the Jews were looking for a chance to put him to death.
2 Amma sa’ad da Bikin Tabanakul na Yahudawa ya yi kusa,
But the feast of the Jews, the feast of tents, was near.
3 sai’yan’uwan Yesu suka ce masa, “Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi.
So his brothers said to him, Go away from here into Judaea so that your disciples may see the works which you do.
4 Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya.”
Because no man does things secretly if he has a desire that men may have knowledge of him. If you do these things, let yourself be seen by all men.
5 Domin ko’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.
For even his brothers had no belief in him.
6 Saboda haka Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna; amma a gare ku kowane lokaci daidai ne.
Jesus said to them, My time is still to come, but any time is good for you.
7 Duniya ba za tă iya ƙinku ba, amma ni take ƙi domin ina shaida cewa ayyukanta mugaye ne.
It is not possible for you to be hated by the world; but I am hated by it, because I give witness that what it does is evil.
8 Ku ku tafi Bikin, ba zan haura zuwa wannan Bikin ba yanzu, domin lokacina bai yi ba tukuna.”
Go you up to the feast: I am not going up now to the feast because my time has not fully come.
9 Da ya faɗa haka, sai ya dakata a Galili.
Having said these things to them, he still kept in Galilee.
10 Amma fa, bayan’yan’uwansa suka tafi Bikin, shi ma ya tafi, ba a fili ba, amma a ɓoye.
But after his brothers had gone up to the feast, then he went up, not publicly, but in secret.
11 A Bikin kuwa, Yahudawa suka yi ta nemansa, suna cewa, “Ina mutumin yake?”
At the feast the Jews were looking for him and saying, Where is he?
12 A cikin taron kuwa aka yi ta raɗe-raɗe game da shi. Waɗansu suka ce, “Shi mutumin kirki ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ai, ruɗin mutane yake.”
And there was much discussion about him among the mass of the people. Some said, He is a good man; but others said, No, he is giving people false ideas.
13 Amma ba wanda ya ce kome a fili game da shi don tsoron Yahudawa.
But no man said anything about him openly for fear of the Jews.
14 Sai bayan da aka kai tsakiyar Bikin, sa’an nan Yesu ya haura zuwa filin haikali ya fara koyarwa.
Now in the middle of the feast Jesus went up to the Temple and was teaching.
15 Yahudawa suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya wannan mutum ya sami wannan sani haka ba tare da ya yi wani karatu ba?”
Then the Jews were surprised and said, How has this man got knowledge of books? He has never been to school.
16 Yesu ya amsa ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta fito ne daga wurin wanda ya aiko ni.
Jesus gave them this answer: It is not my teaching, but his who sent me.
17 Duk wanda ya zaɓi yin nufin Allah, zai gane ko koyarwata daga Allah ce, ko kuwa don kaina ne nake magana.
If any man is ready to do God's pleasure he will have knowledge of the teaching and of where it comes from — from God or from myself.
18 Mai magana don kansa, neman ɗaukakar kansa yake yi. Amma mai neman ɗaukakar wanda ya aiko shi, shi ne mai gaskiya, ba kuwa rashin gaskiya a gare shi.
The man whose words come from himself is looking for glory for himself, but he who is looking for the glory of him who sent him — that man is true and there is no evil in him.
19 Ashe, ba Musa ba ne ya ba ku Doka? Duk da haka ba ko ɗayanku da yake kiyaye Dokar. Me ya sa kuke nema ku kashe ni?”
Did not Moses give you the law? Even so, not one of you keeps the law. Why have you a desire to put me to death?
20 Taron suka amsa suka ce, “Kana da aljani, wane ne yake so yă kashe ka?”
The people said in answer, You have an evil spirit: who has any desire to put you to death?
21 Yesu ya ce musu, “Na yi abin banmamaki ɗaya, dukanku kuwa kuka yi mamaki.
This was the answer of Jesus: I have done one work and you are all surprised at it.
22 Duk da haka, domin Musa ya bar muku kaciya (ko da yake a gaskiya, ba daga wurin Musa ne ya fito ba, sai dai daga wurin kakannin kakanninku), ga shi kuna yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci.
Moses gave you circumcision — not that it comes from Moses, but from the fathers — and even on the Sabbath you give a child circumcision.
23 To, in za a iya yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci don kada a karya dokar Musa, don me kuke fushi da ni saboda na warkar da mutum a ranar Asabbaci?
If a child is given circumcision on the Sabbath so that the law of Moses may not be broken, why are you angry with me because I made a man completely well on the Sabbath?
24 Ku daina yin shari’a bisa ga ganin ido, sai dai ku yi shari’a bisa ga adalci.”
Let not your decisions be based on what you see, but on righteousness.
25 A nan ne fa waɗansu mutane daga Urushalima suka fara tambaya suna cewa, “Ashe, ba wannan mutum ne suke nema su kashe ba?
Then some of the people of Jerusalem said, Is not this the man whose death is desired?
26 Ga shi nan yana magana a fili, su kuma ba su ce masa uffam ba. Ko hukumomi sun yarda cewa shi ne Kiristi?
And here he is talking openly and they say nothing to him! Is it possible that the rulers have knowledge that this is truly the Christ?
27 Mun dai san inda mutumin nan ya fito; amma sa’ad da Kiristi ya zo ba wanda zai san inda ya fito.”
However, it is clear to us where this man comes from: but when the Christ comes no one will have knowledge where he comes from.
28 Yesu yana cikin koyarwa a filin haikali ke nan, sai ya ɗaga murya ya ce, “I, kun san ni, kun kuma san inda na fito. Ban zo don kaina ba, sai dai shi da ya aiko ni mai gaskiya ne. Ba ku san shi ba,
Then, when he was teaching in the Temple, Jesus said with a loud voice, You have knowledge of me and you have knowledge of where I come from; and I have not come of myself; but there is One who has sent me; he is true, but you have no knowledge of him.
29 amma na san shi, domin ni daga wurinsa ne, kuma shi ya aiko ni.”
I have knowledge of him because I came from him and he sent me.
30 Da jin haka, sai suka yi ƙoƙari su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi, don lokacinsa bai yi ba tukuna.
Then they had a desire to take him: but no man put hands on him because his hour was still to come.
31 Duk da haka, da yawa a cikin taron suka ba da gaskiya gare shi. Suka ce, “Sa’ad da Kiristi ya zo, zai yi abubuwan banmamaki fiye da na wannan mutum ne?”
And numbers of the people had belief in him, and they said, When the Christ comes will he do more signs than this man has done?
32 Farisiyawa suka ji taron suna raɗe-raɗen waɗannan abubuwa game da shi. Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka aiki masu gadin haikalin su kama shi.
This discussion of the people came to the ears of the Pharisees; and the chief priests and the Pharisees sent servants to take him.
33 Sai Yesu ya ce, “Ina tare da ku na ɗan ƙanƙanin lokaci ne kawai, sa’an nan zan koma wurin wanda ya aiko ni.
Then Jesus said, I will be with you a little longer and then I go to him who sent me.
34 Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba; inda nake kuwa, ba za ku iya zuwa ba.”
You will be looking for me, and you will not see me: and where I am you may not come.
35 Sai Yahudawa suka ce wa juna, “Ina mutumin nan yake niyyar tafiya da ba za mu iya samunsa ba? Zai je wurin mutanenmu da suke zaune warwatse a cikin Hellenawa, yă kuma koya wa Hellenawa ne?
So the Jews said among themselves, To what place is he going where we will not see him? will he go to the Jews living among the Greeks and become the teacher of the Greeks?
36 Me yake nufi da ya ce, ‘Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba,’ da kuma ‘Inda nake, ba za ku iya zuwa ba’?”
What is this saying of his, You will be looking for me and will not see me, and where I am you may not come?
37 A rana ta ƙarshe kuma mafi girma ta Bikin, Yesu ya tsaya ya yi magana da babbar murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa, yă zo wurina yă sha.
On the last day, the great day of the feast, Jesus got up and said in a loud voice, If any man is in need of drink let him come to me and I will give it to him.
38 Duk wanda ya gaskata da ni, kamar yadda Nassi ya ce, kogunan ruwa masu rai za su gudana daga cikinsa.”
He who has faith in me, out of his body, as the Writings have said, will come rivers of living water.
39 Da wannan yana nufin Ruhu ke nan, wanda waɗanda suka gaskata da shi za su karɓa daga baya. Har yă zuwa wannan lokaci ba a ba da Ruhu ba tukuna, da yake ba a riga an ɗaukaka Yesu ba.
This he said of the Spirit which would be given to those who had faith in him: the Spirit had not been given then, because the glory of Jesus was still to come.
40 Da jin kalmominsa, waɗansu mutane suka ce, “Ba shakka, mutumin nan shi ne Annabin.”
When these words came to their ears, some of the people said, This is certainly the prophet.
41 Waɗansu suka ce, “Shi ne Kiristi.” Waɗansu har wa yau suka ce, “Yaya Kiristi zai fito daga Galili?
Others said, This is the Christ. But others said, Not so; will the Christ come from Galilee?
42 Nassi bai ce Kiristi zai fito daga zuriyar Dawuda, daga kuma Betlehem garin da Dawuda ya zauna ba?”
Do not the Writings say that the Christ comes of the seed of David and from Beth-lehem, the little town where David was?
43 Sai mutanen suka rabu saboda Yesu.
So there was a division among the people because of him.
44 Waɗansu suka so su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi.
And some of them had a desire to take him; but no man put hands on him.
45 A ƙarshe masu gadin haikali suka koma wurin manyan firistocin da Farisiyawa, waɗanda suka tambaye su cewa, “Don me ba ku kawo shi nan ba?”
Then the servants went back to the chief priests and Pharisees, who said to them, Why have you not got him with you?
46 Sai masu gadin suka ce, “Kai, babu wanda ya taɓa magana kamar wannan mutum.”
The servants made answer, No man ever said things like this man.
47 Sai Farisiyawa suka amsa cikin fushi suka ce, “Af, kuna nufi har da ku ma ya ruɗe ku ke nan?
Then the Pharisees said to them, Have you, like the others, been given false ideas?
48 Akwai wani daga cikin masu mulki ko cikin Farisiyawan da ya gaskata da shi?
Have any of the rulers belief in him, or any one of the Pharisees?
49 A’a! Sai dai wannan taron da ba su san kome game da Doka ba, la’anannu ne.”
But these people who have no knowledge of the law are cursed.
50 Nikodimus, wanda ya je wurin Yesu dā, wanda kuma yake ɗayansu ya ce,
Nicodemus — he who had come to Jesus before, being himself one of them — said to them,
51 “Ashe, dokarmu takan hukunta mutum ba tare da an fara ji daga bakinsa game da abin da yake yi ba?”
Is a man judged by our law before it has given him a hearing and has knowledge of what he has done?
52 Sai suka amsa suka ce, “Kai ma daga Galili ne? Bincika ka gani, za ka iske cewa ba annabin da zai fito daga Galili.”
This was their answer: And do you come from Galilee? Make search and you will see that no prophet comes out of Galilee.
53 Sai kowannensu ya koma gidansa.
[And every man went to his house;

< Yohanna 7 >