< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
And Job, responding, said:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Truly, I know that it is so, and that man cannot be justified compared with God.
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
If he chooses to contend with him, he is not able to respond to him once out of a thousand times.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
He is understanding in heart and mighty in strength; who has resisted him and yet had peace?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
He has moved mountains, and those whom he overthrew in his fury did not know it.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
He shakes the earth out of its place and its pillars tremble.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
He commands the sun and it does not rise, and he closes the stars as if under a seal.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
He alone extends the heavens, and he walks upon the waves of the sea.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
He fashions Arcturus, and Orion, and Hyades, and the interior of the south.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
He accomplishes great and incomprehensible and miraculous things, which cannot be numbered.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
If he approaches me, I will not see him; if he departs, I will not understand.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
If he suddenly should question, who will answer him? Or who can say, “Why did you do so?”
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
God, whose wrath no one is able to resist, and under whom they bend who carry the world,
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
what am I then, that I should answer him and exchange words with him?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
And if I now have any justice, I will not respond, but will beseech my judge.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
And if he should listen to me when I call, I would not believe that he had heard my voice.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
For he will crush me in a whirlwind and multiply my wounds, even without cause.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
He does not permit my spirit to rest, and he fills me with bitterness.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
If strength is sought, he is most strong; if equity in judgment, no one would dare to give testimony for me.
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
If I wanted to justify myself, my own mouth will condemn me; if I would reveal my innocence, he would prove me depraved.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
And if I now became simple, my soul would be ignorant even of this, and my life would weary me.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
There is one thing that I have said: both the innocent and the impious he consumes.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
If he scourges, let him kill all at once, and not laugh at the punishment of the innocent.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
Since the earth has been given into the hand of the impious, he covers the face of its judges; for if it is not him, then who is it?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
My days have been swifter than a messenger; they have fled and have not seen goodness.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
They have passed by like ships carrying fruits, just like an eagle flying to food.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
If I say: “By no means will I speak this way.” I change my face and I am tortured with sorrow.
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
I have dreaded all my works, knowing that you did not spare the offender.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Yet, if I am also just as impious, why have I labored in vain?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
If I had been washed with snow-like waters, and my hands were shining like the cleanest thing,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
yet you would plunge me in filth, and my own garments would abhor me.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
For even I would not answer a man who were like myself, nor one who could be heard with me equally in judgment.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
There is no one who could both prevail in argument and in placing his hand between the two.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Let him take his staff away from me, and let not the fear of him terrify me.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
I will speak and I will not fear him, for in fearfulness I am not able to respond.

< Ayuba 9 >