< Ayuba 7 >

1 “Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
"Isn't a man forced to labor on earth? Aren't his days like the days of a hired hand?
2 Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
As a servant who earnestly desires the shadow, as a hireling who looks for his wages,
3 Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
so am I made to possess months of misery, wearisome nights are appointed to me.
4 Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
When I lie down, I say, 'When shall I arise, and the night be gone?' I toss and turn until the dawning of the day.
5 Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
My flesh is clothed with worms and clods of dust. My skin closes up, and breaks out afresh.
6 “Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
My days are swifter than a weaver's shuttle, and are spent without hope.
7 Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
Oh remember that my life is a breath. My eye shall no more see good.
8 Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
The eye of him who sees me shall see me no more. Your eyes shall be on me, but I shall not be.
9 Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol h7585)
As the cloud is consumed and vanishes away, so he who goes down to Sheol shall come up no more. (Sheol h7585)
10 Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
He shall return no more to his house, neither shall his place know him any more.
11 “Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
"Therefore I will not keep silent. I will speak in the anguish of my spirit. I will complain in the bitterness of my soul.
12 Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
Am I a sea, or a sea monster, that you put a guard over me?
13 Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
When I say, 'My bed shall comfort me. My couch shall ease my complaint;'
14 duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
then you scare me with dreams, and terrify me through visions:
15 Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
so that my soul chooses strangling, death rather than my bones.
16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
I loathe my life. I do not want to live forever. Leave me alone, for my days are but a breath.
17 “Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
What is man, that you should magnify him, that you should set your mind on him,
18 har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
that you should visit him every morning, and test him every moment?
19 Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
How long will you not look away from me, nor leave me alone until I swallow down my spittle?
20 In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
If I have sinned, what do I do to you, you watcher of men? Why have you set me as a mark for you, so that I am a burden to myself?
21 Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
Why do you not pardon my disobedience, and take away my iniquity? For now shall I lie down in the dust. You will seek me diligently, but I shall not be."

< Ayuba 7 >