< Ayuba 7 >

1 “Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
[Is there] not an appointed time to man upon earth? [are not] his days also like the days of an hireling?
2 Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
As a servant earnestly desireth the shadow, and as an hireling looketh for [the reward of] his work:
3 Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
So am I made to possess months of vanity, and wearisome nights are appointed to me.
4 Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
When I lie down, I say, When shall I arise, and the night be gone? and I am full of tossings to and fro unto the dawning of the day.
5 Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
My flesh is clothed with worms and clods of dust; my skin is broken, and become loathsome.
6 “Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
My days are swifter than a weaver’s shuttle, and are spent without hope.
7 Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
O remember that my life [is] wind: mine eye shall no more see good.
8 Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
The eye of him that hath seen me shall see me no [more: ] thine eyes [are] upon me, and I [am] not.
9 Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol h7585)
[As] the cloud is consumed and vanisheth away: so he that goeth down to the grave shall come up no [more]. (Sheol h7585)
10 Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
He shall return no more to his house, neither shall his place know him any more.
11 “Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
Therefore I will not refrain my mouth; I will speak in the anguish of my spirit; I will complain in the bitterness of my soul.
12 Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
[Am] I a sea, or a whale, that thou settest a watch over me?
13 Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
When I say, My bed shall comfort me, my couch shall ease my complaint;
14 duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
Then thou scarest me with dreams, and terrifiest me through visions:
15 Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
So that my soul chooseth strangling, [and] death rather than my life.
16 Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
I loathe [it; ] I would not live alway: let me alone; for my days [are] vanity.
17 “Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
What [is] man, that thou shouldest magnify him? and that thou shouldest set thine heart upon him?
18 har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
And [that] thou shouldest visit him every morning, [and] try him every moment?
19 Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
How long wilt thou not depart from me, nor let me alone till I swallow down my spittle?
20 In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
I have sinned; what shall I do unto thee, O thou preserver of men? why hast thou set me as a mark against thee, so that I am a burden to myself?
21 Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
And why dost thou not pardon my transgression, and take away mine iniquity? for now shall I sleep in the dust; and thou shalt seek me in the morning, but I [shall] not [be].

< Ayuba 7 >