< Ayuba 6 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa,
Respondens autem Iob, dixit:
2 “Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
Utinam appenderentur peccata mea, quibus iram merui: et calamitas, quam patior, in statera.
3 Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
Quasi arena maris hæc gravior appareret: unde et verba mea dolore sunt plena:
4 Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
Quia sagittæ Domini in me sunt, quarum indignatio ebibit spiritum meum, et terrores Domini militant contra me.
5 Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
Numquid rugiet onager cum habuerit herbam? aut mugiet bos cum ante præsepe plenum steterit?
6 Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
Aut poterit comedi insulsum, quod non est sale conditum? aut potest aliquis gustare, quod gustatum affert mortem?
7 Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
Quæ prius nolebat tangere anima mea, nunc præ angustia, cibi mei sunt.
8 “Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
Quis det ut veniat petitio mea: et quod expecto, tribuat mihi Deus?
9 wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
Et qui cœpit, ipse me conterat: solvat manum suam, et succidat me?
10 Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
Et hæc mihi sit consolatio ut affligens me dolore, non parcat, nec contradicam sermonibus Sancti.
11 “Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
Quæ est enim fortitudo mea ut sustineam? aut quis finis meus, ut patienter agam?
12 Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
Nec fortitudo lapidum fortitudo mea, nec caro mea ænea est.
13 Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
Ecce, non est auxilium mihi in me, et necessarii quoque mei recesserunt a me.
14 “Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
Qui tollit ab amico suo misericordiam, timorem Domini derelinquit.
15 Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
Fratres mei præterierunt me, sicut torrens qui raptim transit in convallibus.
16 kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
Qui timent pruinam, irruet super eos nix.
17 amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
Tempore, quo fuerint dissipati, peribunt: et ut incaluerit, solventur de loco suo.
18 Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
Involutæ sunt semitæ gressuum eorum: ambulabunt in vacuum, et peribunt.
19 Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
Considerate semitas Thema, itinera Saba, et expectate paulisper.
20 Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
Confusi sunt, quia speravi: venerunt quoque usque ad me, et pudore cooperti sunt.
21 Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
Nunc venistis: et modo videntes plagam meam timetis.
22 Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
Numquid dixi: Afferte mihi, et de substantia vestra donate mihi?
23 ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
Vel, Liberate me de manu hostis, et de manu robustorum eruite me?
24 “Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
Docete me, et ego tacebo: et siquid forte ignoravi, instruite me.
25 Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
Quare detraxistis sermonibus veritatis, cum e vobis nullus sit qui possit arguere me?
26 Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
Ad increpandum tantum eloquia concinnatis, et in ventum verba profertis.
27 Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
Super pupillum irruitis, et subvertere nitimini amicum vestrum.
28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
Verumtamen quod cœpistis explete: præbete aurem, et videte an mentiar.
29 Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Respondete obsecro absque contentione: et loquentes id quod iustum est, iudicate.
30 Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?
Et non invenietis in lingua mea iniquitatem, nec in faucibus meis stultitia personabit.

< Ayuba 6 >