< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
“Do you know the time when the mountain goats give birth? Do you watch when the doe bears fawns?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Can you count the months that they fulfill? Or do you know the time when they give birth?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
They bow themselves. They bear their young. They end their labor pains.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Their young ones become strong. They grow up in the open field. They go out, and don’t return again.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
“Who has set the wild donkey free? Or who has loosened the bonds of the swift donkey,
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
whose home I have made the wilderness, and the salt land his dwelling place?
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
He scorns the tumult of the city, neither does he hear the shouting of the driver.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
The range of the mountains is his pasture. He searches after every green thing.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
“Will the wild ox be content to serve you? Or will he stay by your feeding trough?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Can you hold the wild ox in the furrow with his harness? Or will he till the valleys after you?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Will you trust him, because his strength is great? Or will you leave to him your labor?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Will you confide in him, that he will bring home your seed, and gather the grain of your threshing floor?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
“The wings of the ostrich wave proudly, but are they the feathers and plumage of love?
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
For she leaves her eggs on the earth, warms them in the dust,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
and forgets that the foot may crush them, or that the wild animal may trample them.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
She deals harshly with her young ones, as if they were not hers. Though her labor is in vain, she is without fear,
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
because God has deprived her of wisdom, neither has he imparted to her understanding.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
When she lifts up herself on high, she scorns the horse and his rider.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
“Have you given the horse might? Have you clothed his neck with a quivering mane?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Have you made him to leap as a locust? The glory of his snorting is awesome.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
He paws in the valley, and rejoices in his strength. He goes out to meet the armed men.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
He mocks at fear, and is not dismayed, neither does he turn back from the sword.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
The quiver rattles against him, the flashing spear and the javelin.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
He eats up the ground with fierceness and rage, neither does he stand still at the sound of the trumpet.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
As often as the trumpet sounds he snorts, ‘Aha!’ He smells the battle afar off, the thunder of the captains, and the shouting.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
“Is it by your wisdom that the hawk soars, and stretches her wings toward the south?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Is it at your command that the eagle mounts up, and makes his nest on high?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
On the cliff he dwells and makes his home, on the point of the cliff and the stronghold.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
From there he spies out the prey. His eyes see it afar off.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
His young ones also suck up blood. Where the slain are, there he is.”

< Ayuba 39 >