< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
[Say] if you know the time of the bringing forth of the wild goats of the rock, and [if] you have marked the calving of the hinds:
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
and [if] you has have numbered the full months of their being with young, and [if] you have relieved their pangs:
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
and have reared their young without fear; and will you loosen their pangs?
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Their young will break forth; they will be multiplied with offspring: [their young] will go forth, and will not return to them.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
And who is he that sent forth the wild ass free? and who loosed his bands?
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
whereas I made his habitation the wilderness, and the salt land his coverts.
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
He laughs to scorn the multitude of the city, and hears not the chiding of the tax-gatherer.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
He will survey the mountains [as] his pasture, and he seeks after every green thing.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
And will the unicorn be willing to serve you, or to lie down at your manger?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
And will you bind his yoke with thongs, or will he plow furrows for you in the plain?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
And do you trust him, because his strength is great? and will you commit your works to him?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
And will you believe that he will return to you your seed, and bring [it] in [to] your threshing floor?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
The peacock has a beautiful wing: if the stork and the ostrich conceive, [it is worthy of notice],
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
for [the ostrich] will leave her eggs in the ground, and warm them on the dust,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
and has forgotten that the foot will scatter them, and the wild beasts of the field trample them.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
She has hardened [herself] against her young ones, as though [she bereaved] not herself: she labors in vain without fear.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
For God has withholden wisdom from her, and not given her a portion in understanding.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
In her season she will lift herself on high; she will scorn the horse and his rider.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Hast you invested the horse with strength, and clothed his neck with terror?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
And have you clad him in perfect armor, and made his breast glorious with courage?
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
He paws exulting in the plain, and goes forth in strength into the plain.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
He laughs to scorn a king as he meets him, and will by no means turn back from the sword.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
The bow and sword resound against him; and [his] rage will swallow up the ground:
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
and he will not believe until the trumpet sounds.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
And when the trumpet sounds, he says, Aha! and afar off he smells the war with prancing and neighing.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
And does the hawk remain steady by your wisdom, having spread out her wings unmoved, looking toward the region of the south?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
And does the eagle rise at your command, and the vulture remain sitting over his nest,
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
on a crag of a rock, and in a secret [place]?
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
Thence he seeks food, his eyes observe from far.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
And his young ones roll themselves in blood, and wherever the carcasses may be, immediately they are found.

< Ayuba 39 >