< Ayuba 37 >

1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
“Yes, at this my heart trembles, and is moved out of its place.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Hear, oh, hear the noise of his voice, the sound that goes out of his mouth.
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
He sends it out under the whole sky, and his lightning to the ends of the earth.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
After it a voice roars. He thunders with the voice of his majesty. He doesn’t hold back anything when his voice is heard.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
God thunders marvelously with his voice. He does great things, which we can’t comprehend.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
For he says to the snow, ‘Fall on the earth,’ likewise to the shower of rain, and to the showers of his mighty rain.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
He seals up the hand of every man, that all men whom he has made may know it.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
Then the animals take cover, and remain in their dens.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
Out of its room comes the storm, and cold out of the north.
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
By the breath of God, ice is given, and the width of the waters is frozen.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Yes, he loads the thick cloud with moisture. He spreads abroad the cloud of his lightning.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
It is turned around by his guidance, that they may do whatever he commands them on the surface of the habitable world,
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
whether it is for correction, or for his land, or for loving kindness, that he causes it to come.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
“Listen to this, Job. Stand still, and consider the wondrous works of God.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
Do you know how God controls them, and causes the lightning of his cloud to shine?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
Do you know the workings of the clouds, the wondrous works of him who is perfect in knowledge?
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
You whose clothing is warm when the earth is still by reason of the south wind?
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
Can you, with him, spread out the sky, which is strong as a cast metal mirror?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Teach us what we will tell him, for we can’t make our case by reason of darkness.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
Will it be told him that I would speak? Or should a man wish that he were swallowed up?
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
Now men don’t see the light which is bright in the skies, but the wind passes, and clears them.
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
Out of the north comes golden splendor. With God is awesome majesty.
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
We can’t reach the Almighty. He is exalted in power. In justice and great righteousness, he will not oppress.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
Therefore men revere him. He doesn’t regard any who are wise of heart.”

< Ayuba 37 >