< Ayuba 31 >

1 “Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
I made couenaunt with myn iyen, that Y schulde not thenke of a virgyn.
2 Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
For what part schulde God aboue haue in me, and eritage Almyyti God of hiye thingis?
3 Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
Whether perdicioun is not to a wickid man, and alienacioun of God is to men worchynge wickidnesse?
4 Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Whether he biholdith not my weies, and noumbrith alle my goyngis?
5 “In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
If Y yede in vanyte, and my foot hastide in gile,
6 Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
God weie me in a iust balaunce, and knowe my symplenesse.
7 In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
If my step bowide fro the weie; if myn iye suede myn herte, and a spotte cleuede to myn hondis;
8 bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
sowe Y, and another ete, and my generacioun be drawun out bi the root.
9 “In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
If myn herte was disseyued on a womman, and if Y settide aspies at the dore of my frend; my wijf be the hoore of anothir man,
10 sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
and othir men be bowid doun on hir.
11 Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
For this is vnleueful, and the moost wickidnesse.
12 Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
Fier is deourynge `til to wastyng, and drawynge vp bi the roote alle generaciouns.
13 “In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
If Y dispiside to take doom with my seruaunt and myn hand mayde, whanne thei stryueden ayens me.
14 me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
What sotheli schal Y do, whanne God schal rise to deme? and whanne he schal axe, what schal Y answere to hym?
15 Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Whether he, that wrouyte also hym, made not me in the wombe, and o God formede me in the wombe?
16 “In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
If Y denyede to pore men that, that thei wolden, and if Y made the iyen of a wydewe to abide;
17 in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
if Y aloone eet my mussel, and a faderles child eet not therof;
18 amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
for merciful doyng encreesside with me fro my yong childhed, and yede out of my modris wombe with me;
19 In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
if Y dispiside a man passynge forth, for he hadde not a cloth, and a pore man with out hilyng;
20 kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
if hise sidis blessiden not me, and was not maad hoot of the fleeces of my scheep;
21 in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
if Y reiside myn hond on a fadirles child, yhe, whanne Y siy me the hiyere in the yate;
22 bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
my schuldre falle fro his ioynt, and myn arm with hise boonys be al to-brokun.
23 Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
For euere Y dredde God, as wawis wexynge gret on me; and `Y myyte not bere his birthun.
24 “In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
If Y gesside gold my strengthe, and if Y seide to purid gold, Thou art my trist;
25 in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
if Y was glad on my many ritchessis, and for myn hond foond ful many thingis;
26 In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
if Y siy the sunne, whanne it schynede, and the moone goynge clereli;
27 zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
and if myn herte was glad in priuyte, and if Y kisside myn hond with my mouth;
28 Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
which is the moost wickidnesse, and deniyng ayens hiyeste God;
29 “In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
if Y hadde ioye at the fallyng of hym, that hatide me, and if Y ioide fulli, that yuel hadde founde hym;
30 ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
for Y yaf not my throte to do synne, that Y schulde asaile and curse his soule;
31 in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
if the men of my tabernacle seiden not, Who yyueth, that we be fillid of hise fleischis? a pilgryme dwellide not with outforth;
32 Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
my dore was opyn to a weiegoere;
33 in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
if Y as man hidde my synne, and helide my wickidnesse in my bosum;
34 domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
if Y dredde at ful greet multitude, and if dispisyng of neyyboris made me aferd; and not more Y was stille, and yede not out of the dore;
35 (“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
who yyueth an helpere to me, that Almyyti God here my desire? that he that demeth,
36 Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
write a book, that Y bere it in my schuldre, and cumpasse it as a coroun to me?
37 Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
Bi alle my degrees Y schal pronounce it, and Y schal as offre it to the prynce.
38 “In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
If my lond crieth ayens me, and hise forewis wepen with it;
39 in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
if Y eet fruytis therof with out money, and Y turmentide the soule of erthetileris of it;
40 bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.
a brere growe to me for wheete, and a thorn for barli.

< Ayuba 31 >