< Ayuba 25 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then Bildad the Shuhite answered,
2 “Mulki na Allah ne, dole a ji tsoronsa; yana tafiyar da kome yadda ya kamata a cikin sama.
“Dominion and fear are with him. He makes peace in his high places.
3 Za a iya ƙirga rundunarsa? A kan wane ne ba ya haska haskensa?
Can his armies be counted? On whom does his light not arise?
4 Ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah? Ta yaya mutumin da mace ta haifa zai zama mai tsarki?
How then can man be just with God? Or how can he who is born of a woman be clean?
5 In har wata da taurari ba su da tsarki a idanunsa,
Behold, even the moon has no brightness, and the stars are not pure in his sight;
6 mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah!”
How much less man, who is a worm, and the son of man, who is a worm!”

< Ayuba 25 >