< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then Job answered and said:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Hear diligently my speech; and let this be your consolations.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Suffer me, that I may speak; and after that I have spoken, mock on.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
As for me, is my complaint to man? Or why should I not be impatient?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Turn unto me, and be astonished, and lay your hand upon your mouth.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Even when I remember I am affrighted, and horror hath taketh hold on my flesh.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Wherefore do the wicked live, become old, yea, wax mighty in power?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Their seed is established in their sight with them, and their offspring before their eyes.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Their houses are safe, without fear, neither is the rod of God upon them.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Their bull gendereth, and faileth not; their cow calveth, and casteth not her calf.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
They send forth their little ones like a flock, and their children dance.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
They sing to the timbrel and harp, and rejoice at the sound of the pipe.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
They spend their days in prosperity, and peacefully they go down to the grave. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Yet they said unto God: 'Depart from us; for we desire not the knowledge of Thy ways.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
What is the Almighty, that we should serve Him? And what profit should we have, if we pray unto Him?' —
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Lo, their prosperity is not in their hand; the counsel of the wicked is far from me.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
How oft is it that the lamp of the wicked is put out? that their calamity cometh upon them? that He distributeth pains in His anger?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
That they are as stubble before the wind, and as chaff that the storm stealeth away?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
'God layeth up his iniquity for his children!' — let Him recompense it unto himself, that he may know it.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Let his own eyes see his destruction, and let him drink of the wrath of the Almighty.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
For what pleasure hath he in his house after him? seeing the number of his months is determined.
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Shall any teach God knowledge? seeing it is He that judgeth those that are high.
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
One dieth in his full strength, being wholly at ease and quiet;
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
His pails are full of milk, and the marrow of his bones is moistened.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
And another dieth in bitterness of soul, and hath never tasted of good.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
They lie down alike in the dust, and the worm covereth them.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Behold, I know your thoughts, and the devices which ye wrongfully imagine against me.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
For ye say: 'Where is the house of the prince? And where is the tent wherein the wicked dwelt?'
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Have ye not asked them that go by the way; and will ye misdeem their tokens,
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
That the evil man is reserved to the day of calamity, that they are led forth to the day of wrath?
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
But who shall declare his way to his face? And who shall repay him what he hath done?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
For he is borne to the grave, and watch is kept over his tomb.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
The clods of the valley are sweet unto him, and all men draw after him, as there were innumerable before him.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
How then comfort ye me in vain? And as for your answers, there remaineth only faithlessness?

< Ayuba 21 >