< Ayuba 19 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then Job answered and said,
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
How long will ye vex my soul, and destroy me with words? only know that the Lord has dealt with me thus.
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
Ye speak against me; ye do not feel for me, but bear hard upon me.
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
Yea verily, I have erred in truth, (but the error abides with myself) in having spoken words which it was not right [to speak]; and my words err, and are unreasonable.
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
But alas! for ye magnify yourselves against me, and insult me with reproach.
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
Know then that it is the Lord that has troubled [me], and has raised his bulwark against me.
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
Behold, I laugh at reproach; I will not speak: [or] I will cry out, but [there is] nowhere judgment.
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
I am fenced round about, and can by no means escape: he has set darkness before my face.
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
And he has stripped me of my glory, and has taken the crown from my head.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
He has torn me around about, and I am gone: and he has cut off my hope like a tree.
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
And he has dreadfully handled me in anger, and has counted me for an enemy.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
His troops also came upon me with one accord, liars in wait compassed my ways.
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
My brethren have stood aloof from me; they have recognized strangers [rather] than me: and my friends have become pitiless.
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
My nearest of kin have not acknowledged me, and they that knew my name, have forgotten me.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
[As for] my household, and my maid-servants, I was a stranger before them.
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
I called my servant, and he hearkened not; and my mouth intreated [him].
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
And I besought my wife, and earnestly intreated the sons of my concubines.
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
But they rejected me for ever; whenever I rise up, they speak against me.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
They that saw me abhorred me: the very persons whom I had loved, rose up against me.
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
My flesh is corrupt under my skin, and my bones are held in [my] teeth.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
Pity me, pity me, O friends; for it is the hand of the Lord that has touched me.
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Wherefore do ye persecute me as also the Lord [does], and are not satisfied with my flesh?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
For oh that my words were written, and that they were recorded in a book forever,
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
with an iron pen and lead, or graven in the rocks!
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
For I know that he is eternal who is about to deliver me,
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
[and] to raise up upon the earth my skin that endures these [sufferings]: for these things have been accomplished to me of the Lord;
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
which I am conscious of in myself, which mine eye has seen, and not another, but all have been fulfilled to me in [my] bosom.
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
But if ye shall also say, What shall we say before him, and [so] find the root of the matter in him?
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
Do ye also beware of deceit: for wrath will come upon transgressors; and then shall they know where their substance is.

< Ayuba 19 >