< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Bvt Iob answered, and said,
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
I haue oft times heard such things: miserable comforters are ye all.
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
Shall there be none ende of wordes of winde? or what maketh thee bold so to answere?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
I could also speake as yee doe: (but woulde God your soule were in my soules stead) I could keepe you company in speaking, and could shake mine head at you,
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
But I woulde strengthen you with my mouth, and the comfort of my lips should asswage your sorowe.
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
Though I speake, my sorow can not be asswaged: though I cease, what release haue I?
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
But now hee maketh mee wearie: O God, thou hast made all my congregation desolate,
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
And hast made me full of wrinkles which is a witnesse thereof, and my leannes ryseth vp in me, testifying the same in my face.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
His wrath hath torne me, and hee hateth me, and gnasheth vpon mee with his teeth: mine enemie hath sharpened his eyes against me.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
They haue opened their mouthes vpon me, and smitten me on the cheeke in reproch; they gather themselues together against me.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
God hath deliuered me to the vniust, and hath made mee to turne out of the way by the hands of the wicked.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
I was in welth, but he hath brought me to nought: he hath taken me by the necke, and beaten me, and set me as a marke for himselfe.
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
His archers compasse mee rounde about: he cutteth my reines, and doth not spare, and powreth my gall vpon the ground.
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
He hath broken me with one breaking vpon another, and runneth vpon me like a gyant.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
I haue sowed a sackcloth vpon my skinne, and haue abased mine horne vnto the dust.
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
My face is withered with weeping, and the shadow of death is vpon mine eyes,
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
Though there be no wickednesse in mine hands, and my prayer be pure.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
O earth, couer not thou my blood, and let my crying finde no place.
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
For lo, now my witnesse is in the heauen, and my record is on hie.
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
My friends speake eloquently against me: but mine eye powreth out teares vnto God.
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
Oh that a man might pleade with God, as man with his neighbour!
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
For the yeeres accounted come, and I shall go the way, whence I shall not returne.

< Ayuba 16 >