< Ayuba 12 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then Job answered,
2 “Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
“No doubt, but you are the people, and wisdom will die with you.
3 Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
But I have understanding as well as you; I am not inferior to you. Yes, who doesn’t know such things as these?
4 “Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
I am like one who is a joke to his neighbor, I, who called on God, and he answered. The just, the blameless man is a joke.
5 Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
In the thought of him who is at ease there is contempt for misfortune. It is ready for them whose foot slips.
6 Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
The tents of robbers prosper. Those who provoke God are secure, who carry their god in their hands.
7 “Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
“But ask the animals now, and they will teach you; the birds of the sky, and they will tell you.
8 Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
Or speak to the earth, and it will teach you. The fish of the sea will declare to you.
9 Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
Who doesn’t know that in all these, Yahweh’s hand has done this,
10 Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
in whose hand is the life of every living thing, and the breath of all mankind?
11 Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
Doesn’t the ear try words, even as the palate tastes its food?
12 Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
With aged men is wisdom, in length of days understanding.
13 “Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
“With God is wisdom and might. He has counsel and understanding.
14 Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
Behold, he breaks down, and it can’t be built again. He imprisons a man, and there can be no release.
15 Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
Behold, he withholds the waters, and they dry up. Again, he sends them out, and they overturn the earth.
16 Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
With him is strength and wisdom. The deceived and the deceiver are his.
17 Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
He leads counselors away stripped. He makes judges fools.
18 Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
He loosens the bond of kings. He binds their waist with a belt.
19 Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
He leads priests away stripped, and overthrows the mighty.
20 Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
He removes the speech of those who are trusted, and takes away the understanding of the elders.
21 Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
He pours contempt on princes, and loosens the belt of the strong.
22 Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
He uncovers deep things out of darkness, and brings out to light the shadow of death.
23 yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
He increases the nations, and he destroys them. He enlarges the nations, and he leads them captive.
24 Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
He takes away understanding from the chiefs of the people of the earth, and causes them to wander in a wilderness where there is no way.
25 Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.
They grope in the dark without light. He makes them stagger like a drunken man.

< Ayuba 12 >