< Ayuba 11 >

1 Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then Zophar, the Naamathite, answered,
2 “Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
“Shouldn’t the multitude of words be answered? Should a man full of talk be justified?
3 Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
Should your boastings make men hold their peace? When you mock, will no man make you ashamed?
4 Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
For you say, ‘My doctrine is pure. I am clean in your eyes.’
5 Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
But oh that God would speak, and open his lips against you,
6 yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
that he would show you the secrets of wisdom! For true wisdom has two sides. Know therefore that God exacts of you less than your iniquity deserves.
7 “Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
“Can you fathom the mystery of God? Or can you probe the limits of the Almighty?
8 Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
They are high as heaven. What can you do? They are deeper than Sheol. What can you know? (Sheol h7585)
9 Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
Its measure is longer than the earth, and broader than the sea.
10 “In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
If he passes by, or confines, or convenes a court, then who can oppose him?
11 Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
For he knows false men. He sees iniquity also, even though he doesn’t consider it.
12 Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
An empty-headed man becomes wise when a man is born as a wild donkey’s colt.
13 “Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
“If you set your heart aright, stretch out your hands toward him.
14 in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
If iniquity is in your hand, put it far away. Don’t let unrighteousness dwell in your tents.
15 shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
Surely then you will lift up your face without spot. Yes, you will be steadfast, and will not fear,
16 Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
for you will forget your misery. You will remember it like waters that have passed away.
17 Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
Life will be clearer than the noonday. Though there is darkness, it will be as the morning.
18 Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
You will be secure, because there is hope. Yes, you will search, and will take your rest in safety.
19 Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
Also you will lie down, and no one will make you afraid. Yes, many will court your favor.
20 Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”
But the eyes of the wicked will fail. They will have no way to flee. Their hope will be the giving up of the spirit.”

< Ayuba 11 >