< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
My soul is weary of my life; I will leave my complaint upon myself; I will speak in the bitterness of my soul.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
I will say to God, Do not condemn me; show me why thou contendest with me.
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Is it good to thee that thou shouldest oppress, that thou shouldest despise the work of thy hands, and shine upon the counsel of the wicked?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Hast thou eyes of flesh? or seest thou as man seeth?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
Are thy days as the days of man? are thy years as man’s days,
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
That thou enquirest after my iniquity, and searchest after my sin?
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Thou knowest that I am not wicked; and there is none that can deliver out of thy hand.
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Thy hands have made me and fashioned me in all my parts; yet thou dost destroy me.
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Remember, I beseech thee, that thou hast made me as the clay; and wilt thou bring me into dust again?
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Hast thou not poured me out as milk, and curdled me like cheese?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
Thou hast clothed me with skin and flesh, and hast fenced me with bones and sinews.
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Thou hast granted me life and favour, and thy care hath preserved my spirit.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
And these things hast thou hid in thy heart: I know that this is with thee.
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
If I sin, then thou markest me, and thou wilt not acquit me from my iniquity.
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
If I be wicked, woe to me; and if I be righteous, yet will I not lift up my head. I am full of confusion; therefore see thou my affliction;
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
For it increaseth. Thou huntest me as a fierce lion: and again thou showest thyself marvellous upon me.
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
Thou renewest thy witnesses against me, and increasest thy indignation upon me; changes and war are against me.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
Why then hast thou brought me forth from the womb? O that I had given up the ghost, and no eye had seen me!
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
I should have been as though I had not been; I should have been carried from the womb to the grave.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Are not my days few? cease then, and let me alone, that I may take comfort a little,
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
Before I go to the place from which I shall not return, even to the land of darkness and the shadow of death;
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
A land of darkness, as darkness itself; and of the shadow of death, without any order, and where the light is as darkness.

< Ayuba 10 >