< Irmiya 44 >

1 Wannan maganata zo wa Irmiya game da dukan Yahudawa masu zama a Masar ta Ƙasa, a Migdol, Tafanes da Memfis, da kuma a Masar ta Bisa.
The word came to Jeremiah concerning all the Judeans who lived in the land of Egypt, the ones staying in Migdol, Tahpanhes, Memphis, and in Upper Egypt:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa kun ga masifa mai girmar da na kawo a kan Urushalima da kuma a kan dukan garuruwan Yahuda. A yau sun zama hamada da kuma kango
“Yahweh of hosts, God of Israel, says, 'You yourselves have seen all the disasters that I brought on Jerusalem and all the cities of Judah. See, they are ruins today. There is no one to live in them.
3 saboda muguntar da suka aikata. Sun tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙone turare da kuma ta wurin bauta wa waɗansu allolin da su ko ku ko kakanninku ba su taɓa sani ba.
This is because of the wicked things they did to offend me by going to burn incense and to worship other gods. These were gods that neither they themselves, nor you, nor your ancestors knew.'
4 Sau da sau na aiki bayina annabawa, waɗanda suka ce, ‘Kada ku yi wannan abin ƙyama da na ƙi!’
So I repeatedly sent all of my servants the prophets to them. I sent them to say, 'Stop doing these abominable things that I hate.'
5 Amma ba su saurara ko su kasa kunne ba; ba su juye daga muguntarsu ko su daina ƙone turare wa waɗansu alloli ba.
But they did not listen. They refused to pay attention or turn from their wickedness in burning incense to other gods.
6 Saboda haka, fushina mai ƙuna ya fāɗo a kan garuruwan Yahuda da kuma titunan Urushalima na kuma mai da su kufai da suke a yau.
So my fury and my wrath were poured out and kindled a fire in the cities of Judah and the streets of Jerusalem. So they became ruins and devastations, as at this present day.'
7 “To, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa don me kuka kawo irin masifa mai girma haka a kanku ta wurin warewa daga Yahuda maza da mata, yara da jarirai, kun kuma bar kanku babu raguwa?
So now Yahweh, the God of hosts and the God of Israel, says this, 'Why are you doing great wickedness against yourselves? Why are you causing yourselves to be cut off from among Judah—men and women, children and babies? No remnant of you will be left.
8 Me ya sa kuka tsokane ni in yi fushi saboda abin da hannuwanku suka yi, kuna ƙone turare wa waɗansu alloli a Masar, inda kuka zo don ku zauna? Za ku hallakar da kanku ku kuma mai da kanku abin la’ana da abin zargi da abin ba’a a cikin dukan al’umman duniya.
By your wickedness you have offended me with the deeds of your hands, by burning incense to other gods in the land of Egypt, where you have gone to live. You have gone there so that you will be destroyed, so that you will be a curse and a reproach among all the nations of the earth.
9 Kun manta mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakuna da sarauniyoyin Yahuda da mugayen ayyukanku, da na matanku a cikin Yahuda da kan titunan Urushalima?
Have you forgotten the wickedness committed by your ancestors and the wickedness committed by the kings of Judah and their wives? Have you forgotten the evil committed by yourselves and your wives in the land of Judah and the streets of Jerusalem?
10 Har yă zuwa yau ba su ƙasƙantar da kansu ko su nuna bangirma, ko su kiyaye dokata da ƙa’idodin da na sa a gabanku da kakanninku ba.
To this day, they still are not humbled. They do not honor my law or decrees that I placed before them and their ancestors, nor do they walk in them.'
11 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa na ƙudura in aukar muku da masifa in kuma hallaka dukan Yahuda.
Therefore Yahweh of hosts, God of Israel, says this, 'See, I am about to set my face against you to bring disaster to you and to destroy all of Judah.
12 Zan ɗauke raguwar Yahuda waɗanda suka ƙudurta su je Masar su zauna a can. Duk za su hallaka a Masar; za su mutu ta wurin takobi ko su mutu da yunwa. Daga ƙarami zuwa babba, za su mutu ta wurin takobi ko yunwa. Za su zama abin zarge da abin tsoro, abin la’ana da abin ba’a.
For I will take the remnant of Judah that has set out to go to the land of Egypt to live there. I will do this so that they will all perish in the land of Egypt. They will fall by sword and famine. From the least to the greatest they will perish by sword and famine. They will die and will become an object of swearing, cursing, reproaching, and a horrible thing.
13 Zan hukunta waɗanda suke zama a Masar da takobi, yunwa da annoba, yadda na hukunta Urushalima.
For I will punish the people inhabiting the land of Egypt just as I punished Jerusalem with the sword, with famine, and with the plague,
14 Babu wani daga raguwar Yahuda wanda ya tafi Masar da zai kuɓuta ko ya tsira har ya komo zuwa ƙasar Yahuda, wadda za su yi marmari su komo su zauna; babu wani da zai komo sai dai’yan gudun hijira.”
so that none of the remnant of Judah who have gone to live in the land of Egypt will escape or survive or return to the land of Judah, to which they desire to return and live; and none of them will return except a few who escaped from there.'”
15 Sai dukan mazan da suka san cewa matansu suna ƙone turare wa waɗansu alloli, tare da dukan matan da suke a nan babban taro, da kuma dukan mutanen da suke zama a Masar ta Ƙasa da ta Bisa, suka ce wa Irmiya,
Then all the men who knew that their wives were burning incense to other gods, and all the women who were in the great assembly, and all the people who were living in Lower and Upper Egypt, answered Jeremiah.
16 “Ba za mu saurari saƙon da ka yi mana magana a sunan Ubangiji ba!
They said, “About the word that you have told us in Yahweh's name—we will not listen to you.
17 Lalle za mu aikata duk abin da muka ce za mu yi. Za mu ƙone turare ga Sarauniyar Sama za mu kuma miƙa hadayun sha gare ta kamar dai yadda mu da kakanninmu, sarakunanmu da fadawanmu muka yi a garuruwan Yahuda da kuma kan titunan Urushalima. A lokacin muna da abinci a yalwace muna kuma da arziki ba mu kuma da wata damuwa.
For we will certainly do all the things that we said we would do—burn incense to the queen of heaven and pour out drink offerings to her just as we, our ancestors, our kings, and our leaders did in the cities of Judah and the streets of Jerusalem. Then we will be filled with food and will prosper, without experiencing any disaster.
18 Amma tun da muka daina ƙone turare ga Sarauniyar Sama da kuma miƙa mata hadayun sha, muka rasa kome muna ta mutuwa ta wurin takobi da yunwa.”
When we refrained from doing these things, not offering incense to the queen of heaven and not pouring out drink offerings to her, we were all suffering poverty and were dying by sword and famine.”
19 Matan suka ƙara da cewa, “Sa’ad da muka ƙone turare ga Sarauniyar Sama muka kuma miƙa mata hadayun sha, mazanmu ba su san muna yin waina kamar siffarta muna kuma miƙa mata hadayun sha ba?”
The women said, “When we were making incense offerings before the queen of heaven and pouring out drink offerings to her, was it against our husbands that we did these things, making cakes in her image and pouring out drink offerings to her?”
20 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutanen, maza da mata, waɗanda suke ba shi amsa,
Then Jeremiah said to all the people—to the men and women, and all the people who answered him—he proclaimed and said,
21 “Ubangiji bai tuna ya kuma yi tunani game da turaren da aka ƙone a garuruwan Yahuda da kan titunan Urushalima wanda ku da kakanninku, sarakunanku da fadawanku da mutanen ƙasar ba ne?
“Did not Yahweh remember the incense that you burned in the cities of Judah and the streets of Jerusalem—you and your ancestors, your kings and leaders, and the people of the land? For Yahweh calls this to mind; it comes to his thoughts.
22 Sa’ad da Ubangiji bai iya jurewa da mugayen ayyukanku da kuma abubuwa banƙyama da kuka aikata ba, sai ƙasarku ta zama abin la’ana da kufai babu mazauna yadda yake a yau.
Then he was no longer able to bear it because of your wicked practices, because of the abominations that you did. Then your land became a desolation, a horror, and a curse so there was no longer an inhabitant as at this present day.
23 Domin kun ƙone turare kuka kuma yi wa Ubangiji zunubi ba ku kuma yi masa biyayya ko ku kiyaye dokarsa ko ƙa’idodinsa ko farillansa ba, wannan masifa ta aukar muku, yadda yanzu kuka gani.”
Because you burned incense and sinned against Yahweh, and because you would not listen to his voice, his law, his statutes, or his covenant decrees, this disaster against you has happened as at this present day.”
24 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane, har da mata, “Ku saurari maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda a Masar.
Then Jeremiah said to all the people and all the women, “Hear the word of Yahweh, all of Judah who are in the land of Egypt.
25 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku da matanku kun nuna ta wurin ayyukanku abin da kuka yi alkawari sa’ad da kuka ce, ‘Lalle za mu yi abin da muka yi alkawari na ƙone turare da kuma miƙa hadayun sha ga Sarauniyar Sama.’ “To, sai ku ci gaba, ku aikata abin da kuka yi alkawari! Ku cika alkawarinku!
Yahweh of hosts, God of Israel, says this, 'You and your wives both have said with your mouths and carried out with your hands what you said, “We will certainly carry out the vows that we made to worship the queen of heaven, to pour out drink offerings to her.” Now fulfill your vows; carry them out.'
26 Amma ku ji maganar Ubangiji, dukan Yahudawan da suke zama a Masar, ‘Na rantse da sunana,’ in ji Ubangiji, ‘cewa babu wani daga Yahuda wanda yake zama a ko’ina a Masar zai ƙara kira bisa sunana ko ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji Mai Iko Duka yana raye.”
So then, hear the word of Yahweh, all of Judah who are staying in the land of Egypt, 'See, I have sworn by my great name—says Yahweh. My name will no longer be called upon by the mouths of any of the men of Judah in all the land of Egypt, you who now say, “As the Lord Yahweh lives.”
27 Gama ina lura da su don lahani, ba alheri ba; mutanen Yahuda da suke a Masar za su hallaka ta wurin takobi da yunwa sai dukansu sun hallaka.
See, I am watching over them for disaster and not for good. Every person of Judah in the land of Egypt will perish by sword and famine until they are all finished.
28 Waɗanda suka kuɓuta wa takobi suka komo zuwa ƙasar Yahuda daga Masar za su zama kima kawai. Sa’an nan dukan raguwar Yahuda waɗanda suka zo don su yi zama a Masar za su san maganar wane ne za tă tabbata, tawa ko tasu.
Then the survivors of the sword will return from the land of Egypt to the land of Judah, only a small number of them. So all the remnant of Judah who went to the land of Egypt to live there will know whose word will stand—mine or theirs.
29 “‘Wannan zai zama alama a gare ku cewa zan hukunta ku a wannan wuri,’ in ji Ubangiji, ‘saboda ku san cewa barazanata ta lahani a kanku tabbatacce za tă cika.’
This will be the sign for you—this is Yahweh's declaration—that I am setting against you in this place, so that you will know that my words will certainly attack you with disaster.'
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan bayar da Fir’auna Hofra sarkin Masar ga abokan gābansa waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, abokin gāban da ya nemi ransa.’”
Yahweh says this, 'Look, I am about to give Pharaoh Hophra king of Egypt into the hand of his enemies and into the hand of those who seek to kill him. It will the same as when I gave Zedekiah king of Judah into the hand of Nebuchadnezzar king of Babylon, his enemy who sought his life.'”

< Irmiya 44 >