< Irmiya 32 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
The word that came to Jeremiah from the LORD in the tenth year of Zedekiah king of Judah, which was the eighteenth year of Nebuchadrezzar.
2 Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
Now at that time the king of Babylon's army was besieging Jerusalem; and Jeremiah the prophet was shut up in the court of the guard, which was in the king of Judah's house.
3 Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
For Zedekiah king of Judah had shut him up, saying: 'Wherefore dost thou prophesy, and say: Thus saith the LORD: Behold, I will give this city into the hand of the king of Babylon, and he shall take it;
4 Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
and Zedekiah king of Judah shall not escape out of the hand of the Chaldeans, but shall surely be delivered into the hand of the king of Babylon, and shall speak with him mouth to mouth, and his eyes shall behold his eyes;
5 Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
and he shall lead Zedekiah to Babylon, and there shall he be until I remember him, saith the LORD; though ye fight with the Chaldeans, ye shall not prosper?'
6 Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And Jeremiah said: 'The word of the LORD came unto me, saying:
7 Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
Behold, Hanamel, the son of Shallum thine uncle, shall come unto thee, saying: Buy thee my field that is in Anathoth; for the right of redemption is thine to buy it.'
8 “Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
So Hanamel mine uncle's son came to me in the court of the guard according to the word of the LORD, and said unto me: 'Buy my field, I pray thee, that is in Anathoth, which is in the land of Benjamin; for the right of inheritance is thine, and the redemption is thine; buy it for thyself.' Then I knew that this was the word of the LORD.
9 saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
And I bought the field that was in Anathoth of Hanamel mine uncle's son, and weighed him the money, even seventeen shekels of silver.
10 Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
And I subscribed the deed, and sealed it, and called witnesses, and weighed him the money in the balances.
11 Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
So I took the deed of the purchase, both that which was sealed, containing the terms and conditions, and that which was open;
12 na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
and I delivered the deed of the purchase unto Baruch the son of Neriah, the son of Mahseiah, in the presence of Hanamel mine uncle 's son, and in the presence of the witnesses that subscribed the deed of the purchase, before all the Jews that sat in the court of the guard.
13 “A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
And I charged Baruch before them, saying:
14 ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
'Thus saith the LORD of hosts, the God of Israel: Take these deeds, this deed of the purchase, both that which is sealed, and this deed which is open, and put them in an earthen vessel; that they may continue many days.
15 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
For thus saith the LORD of hosts, the God of Israel: Houses and fields and vineyards shall yet again be bought in this land.'
16 “Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
Now after I had delivered the deed of the purchase unto Baruch the son of Neriah, I prayed unto the LORD, saying:
17 “A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
'Ah Lord GOD! behold, Thou hast made the heaven and the earth by Thy great power and by Thy outstretched arm; there is nothing too hard for Thee;
18 Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
who showest mercy unto thousands, and recompensest the iniquity of the fathers into the bosom of their children after them; the great, the mighty God, the LORD of hosts is His name;
19 manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
great in counsel, and mighty in work; whose eyes are open upon all the ways of the sons of men, to give every one according to his ways, and according to the fruit of his doings;
20 Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
who didst set signs and wonders in the land of Egypt, even unto this day, and in Israel and among other men; and madest Thee a name, as at this day;
21 Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
and didst bring forth Thy people Israel out of the land of Egypt with signs, and with wonders, and with a strong hand, and with an outstretched arm, and with great terror;
22 Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
and gavest them this land, which Thou didst swear to their fathers to give them, a land flowing with milk and honey;
23 Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
and they came in, and possessed it; but they hearkened not to Thy voice, neither walked in Thy law; they have done nothing of all that Thou commandedst them to do; therefore Thou hast caused all this evil to befall them;
24 “Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
behold the mounds, they are come unto the city to take it; and the city is given into the hand of the Chaldeans that fight against it, because of the sword, and of the famine, and of the pestilence; and what Thou hast spoken is come to pass; and, behold, Thou seest it.
25 Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
Yet Thou hast said unto me, O Lord GOD: Buy thee the field for money, and call witnesses; whereas the city is given into the hand of the Chaldeans.'
26 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Then came the word of the LORD unto Jeremiah, saying:
27 “Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
'Behold, I am the LORD, the God of all flesh; is there any thing too hard for Me?
28 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
Therefore thus saith the LORD: Behold, I will give this city into the hand of the Chaldeans, and into the hand of Nebuchadrezzar king of Babylon, and he shall take it;
29 Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
and the Chaldeans, that fight against this city, shall come and set this city on fire, and burn it, with the houses, upon whose roofs they have offered unto Baal, and poured out drink-offerings unto other gods, to provoke Me.
30 “Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
For the children of Israel and the children of Judah have only done that which was evil in My sight from their youth; for the children of Israel have only provoked Me with the work of their hands, saith the LORD.
31 Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
For this city hath been to Me a provocation of Mine anger and of My fury from the day that they built it even unto this day, that I should remove it from before My face;
32 Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
because of all the evil of the children of Israel and of the children of Judah, which they have done to provoke Me, they, their kings, their princes, their priests, and their prophets, and the men of Judah, and the inhabitants of Jerusalem.
33 Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
And they have turned unto Me the back, and not the face; and though I taught them, teaching them betimes and often, yet they have not hearkened to receive instruction.
34 Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
But they set their abominations in the house whereupon My name is called, to defile it.
35 Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
And they built the high places of Baal, which are in the valley of the son of Hinnom, to set apart their sons and their daughters unto Molech; which I commanded them not, neither came it into My mind, that they should do this abomination; to cause Judah to sin.
36 “Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
And now therefore thus saith the LORD, the God of Israel, concerning this city, whereof ye say: It is given into the hand of the king of Babylon by the sword, and by the famine, and by the pestilence:
37 tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
Behold, I will gather them out of all the countries, whither I have driven them in Mine anger, and in My fury, and in great wrath; and I will bring them back unto this place, and I will cause them to dwell safely;
38 Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
and they shall be My people, and I will be their God;
39 Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
and I will give them one heart and one way, that they may fear Me for ever; for the good of them, and of their children after them;
40 Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
and I will make an everlasting covenant with them, that I will not turn away from them, to do them good; and I will put My fear in their hearts, that they shall not depart from Me.
41 Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
Yea, I will rejoice over them to do them good, and I will plant them in this land in truth with My whole heart and with My whole soul.
42 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
For thus saith the LORD: Like as I have brought all this great evil upon this people, so will I bring upon them all the good that I have promised them.
43 Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
And fields shall be bought in this land, whereof ye say: It is desolate, without man or beast; it is given into the hand of the Chaldeans.
44 Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”
Men shall buy fields for money, and subscribe the deeds, and seal them, and call witnesses, in the land of Benjamin, and in the places about Jerusalem, and in the cities of Judah, and in the cities of the hill-country, and in the cities of the Lowland, and in the cities of the South; for I will cause their captivity to return, saith the LORD.'

< Irmiya 32 >