< Irmiya 13 >

1 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
Ainsi m'a parlé Yahweh: " Va t'acheter une ceinture de lin, et pose-là sur tes reins, mais ne la mets pas dans l'eau. "
2 Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
Et je m'achetai la ceinture, selon la parole de Yahweh, et je la mis sur mes reins.
3 Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
La parole de Yahweh me fut adressée une seconde fois, en ces termes:
4 “Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
" Prends la ceinture que tu as achetée et qui est sur tes reins; lève-toi, va vers l'Euphrate, et là tu la cacheras dans une fente de rocher. "
5 Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
J'allai et je la cachai près de l'Euphrate, comme Yahweh me l'avait ordonné.
6 Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
Et, au bout d'un grand nombre de jours, Yahweh me dit: " Lève-toi, va vers l'Euphrate, et là reprends la ceinture que je t'ai commandé d'y cacher ".
7 Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
J'allai vers l'Euphrate, je creusai et je repris la ceinture au lieu où je l'avais cachée; et voilà que la ceinture était perdue, elle n'était plus bonne à rien.
8 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de Yahweh me fut adressée, en ces termes:
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
Ainsi parle Yahweh: C'est ainsi que je perdrai l'orgueil de Juda, et le grand orgueil de Jérusalem.
10 Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
Ce peuple mauvais qui refuse d'écouter mes paroles, qui suit l'opiniâtreté de son cœur et qui va après d'autres dieux pour les servir et les adorer, il sera comme cette ceinture, qui n'est plus bonne à rien.
11 Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
Car, comme la ceinture est attachée aux reins de l'homme, ainsi je m'étais attaché toute la maison d'Israël et toute la maison de Juda, — oracle de Yahweh, afin qu'elles fussent pour moi un peuple, un nom, un honneur et une gloire; mais ils n'ont pas écouté!
12 “Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
Et tu leur diras cette parole: " Ainsi parle Yahweh, Dieu d'Israël: Toute cruche doit être remplie de vin. " Ils te répondront: " Ne savons-nous pas que toute cruche doit être remplie de vin? "
13 Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
Et tu leur diras: " Ainsi parle Yahweh: Je vais remplir tous les habitants de ce pays, et les rois qui sont assis sur le trône de David, les prêtres et les prophètes, et tous les habitants de Jérusalem, d'ivresse.
14 Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
Et je les briserai les uns contre les autres, les pères et les fils ensemble, — oracle de Yahweh; je n'épargnerai pas, je n'aurai pas de compassion, je n'aurai pas de pitié pour ne pas les détruire.
15 Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
Ecoutez, prêtez l'oreille, ne soyez point orgueilleux, car Yahweh a parlé.
16 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
Rendez gloire à Yahweh, votre Dieu, avant que viennent les ténèbres, que vos pieds se heurtent aux montagnes de la nuit, qu'il change en ombre de mort la lumière que vous attendez, et qu'il en fasse une obscurité profonde.
17 Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
Si vous n'écoutez pas cela, mon âme pleurera en secret, à cause de votre orgueil; mes yeux pleureront amèrement, se fondront en larmes, car le troupeau de Jacob sera emmené captif.
18 Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
Dis au roi et à la reine: Asseyez-vous à terre, car elle tombe de votre tête, votre couronne de gloire.
19 Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
Les villes du midi sont fermées, et personne ne les ouvre; Juda tout entier est déporté; la déportation est complète.
20 Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
Lève les yeux et vois ceux qui viennent du septentrion: Où est le troupeau qui t'avait été donné, les brebis qui faisaient ta gloire?
21 Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
Que diras-tu quand Yahweh te donnera pour maîtres ceux que tu as instuits contre toi — tes familiers? Les douleurs ne te saisiront-elles pas, comme une femme qui enfante?
22 In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
Et si tu dis dans ton cœur: " Pourquoi ces malheurs m'arrivent-ils?... " C'est à cause de la multitude de tes iniquités que les pans de ta robe ont été relevés, que tes talons ont été meurtris.
23 Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
Un Ethiopien changera-t-il sa peau, un léopard ses taches? Et vous, pourriez-vous faire le bien, vous qui êtes appris à mal faire?
24 “Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
Je les disperserai comme la paille qui passe, au souffle du vent du désert.
25 Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
Tel est ton sort, la part que je te mesure, — oracle de Yahweh, parce que tu m'as oublié, que tu as mis ta confiance dans le mensonge.
26 Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
Et moi aussi je relèverai les pans de ta robe sur ton visage, et l'on verra ta honte.
27 zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”
Tes adultères, tes hennissements, tes criminelles prostitutions, sur les collines en pleine campagne, toutes tes abominations, je les ai vues. Malheur à toi, Jérusalem! Tu es impure jusques à quand encore?

< Irmiya 13 >