< Ishaya 8 >

1 Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
Yahweh said to me, “Take a large tablet and write on it, 'Maher-Shalal-Hash-Baz.'
2 Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
I will summon faithful witnesses to attest for me, Uriah the priest, and Zechariah son of Jeberekiah.”
3 Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
I went to the prophetess, and she conceived and bore a son. Then Yahweh said to me, “Call his name Maher-Shalal-Hash-Baz.
4 Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
For before the child knows to cry, 'My father,' and, 'My mother,' the riches of Damascus and the plunder of Samaria will be carried away by the king of Assyria.”
5 Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
Yahweh spoke to me again,
6 “Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
“Because this people has refused the gentle waters of Shiloah, and is happy over Rezin and Remaliah's son,
7 saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
therefore the Lord is about to bring up on them the waters of the River, mighty and many, the king of Assyria and all his glory. It will come up over all its channels and overflow its banks.
8 Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
The River will sweep onward into Judah, flooding and passing on, until it reaches to your neck. Its outstretched wings will fill the breadth of your land, Immanuel.”
9 Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
You peoples will be broken to pieces. Listen, all you distant countries: arm yourselves for war and be broken in pieces; arm yourselves and be broken in pieces.
10 Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
Form a plan, but it will not be carried out; issue the command, but it will not be carried out, for God is with us.
11 Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
Yahweh spoke to me, with his strong hand upon me, and warned me not to walk in the way of this people.
12 “Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
Do not call conspiracy anything that this people calls conspiracy, you will not fear what they fear, and do not be terrified.
13 Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
It is Yahweh of hosts whom you will honor as holy; he is the one you must fear, and he is the one you must dread.
14 zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
He will become a sanctuary; but he will be a stone of striking, and a rock of stumbling— for both the houses of Israel, and he will be a trap and a snare to the people of Jerusalem.
15 Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
Many will stumble over it and fall and be broken, and be ensnared and captured.
16 Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
Bind up my testimony, seal the official record, and give it to my disciples.
17 Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
I will wait for Yahweh, who hides his face from the house of Jacob; I will trust in him.
18 Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
See, I and the sons whom Yahweh has given me are for signs and for wonders in Israel from Yahweh of hosts, who lives on Mount Zion.
19 Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
They will say to you, “Consult with the mediums and spiritists,” those who chirp and mutter incantations. But should a people not consult their God? Should they consult the dead on behalf of the living?
20 Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
To the law and to the testimony! If they do not say such things, it is because they have no light of dawn.
21 Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
They will pass through the land greatly distressed and hungry. When they are hungry, they will become angry and curse their king and their God, as they turn their faces upward.
22 Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.
They will look at the earth and see distress, darkness, and oppressive gloom. They will be driven into a land of darkness.

< Ishaya 8 >