< Ishaya 62 >

1 Saboda Sihiyona ba zan yi shiru ba, saboda Urushalima ba zan huta ba, sai adalcinta ya haskaka kamar hasken safiya, cetonta kuma ya haskaka kamar fitila mai haske.
For Zion’s sake I will not hold my peace, and for Jerusalem’s sake I will not rest, until her righteousness shines out like the dawn, and her salvation like a burning lamp.
2 Al’ummai za su ga adalcinki, sarakuna kuma za su ga ɗaukakarki; za a kira ki da sabon suna sunan da bakin Ubangiji zai ambata.
The nations will see your righteousness, and all kings your glory. You will be called by a new name, which Yahweh’s mouth will name.
3 Za ki zama rawanin daraja a hannun Ubangiji, rawanin sarauta a hannun Allahnki.
You will also be a crown of beauty in Yahweh’s hand, and a royal diadem in your God’s hand.
4 Ba za a ƙara ce da ke Yasasshiya ba, ko a kira ƙasarki Kango. Amma za a ce da ke Hefziba ƙasarki kuma Bewula; gama Ubangiji zai ji daɗinki, ƙasarki kuma za tă yi aure.
You will not be called Forsaken any more, nor will your land be called Desolate any more; but you will be called Hephzibah, and your land Beulah; for Yahweh delights in you, and your land will be married.
5 Kamar yadda saurayi kan auri yarinya, haka’ya’yanki maza za su aure ki; kamar kuma yadda ango yakan yi farin ciki da amaryarsa, haka Allahnki zai yi farin ciki da ke.
For as a young man marries a virgin, so your sons will marry you. As a bridegroom rejoices over his bride, so your God will rejoice over you.
6 Na sa matsara a kan katangarki, ya Urushalima; ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Ku da kuke kira bisa sunan Ubangiji, kada ku ba kanku hutu,
I have set watchmen on your walls, Jerusalem. They will never be silent day nor night. You who call on Yahweh, take no rest,
7 kuma kada ku ba shi hutu sai ya kafa Urushalima ya kuma mai da ita yabon duniya.
and give him no rest until he establishes, and until he makes Jerusalem a praise in the earth.
8 Ubangiji ya rantse da hannunsa na dama ta hannunsa kuma mai iko cewa, “Ba zan ƙara ba da hatsinki ya zama abinci ga abokan gābanki ba, baƙi kuma ba za su ƙara shan ruwan inabin wanda kika sha wahala samu ba;
Yahweh has sworn by his right hand, and by the arm of his strength, “Surely I will no more give your grain to be food for your enemies, and foreigners will not drink your new wine, for which you have labored,
9 amma waɗanda suka girbe shi za su ci shi su kuma yabi Ubangiji, waɗanda kuma suka tattara’ya’yan inabi za su sha shi a filayen wurina mai tsarki.”
but those who have harvested it will eat it, and praise Yahweh. Those who have gathered it will drink it in the courts of my sanctuary.”
10 Ku wuce, ku wuce ƙofofi! Ku shirya hanya saboda mutane. Ku gina, ku gina babbar hanya! Ku kawar da duwatsu. Ku ɗaga tuta saboda al’ummai.
Go through, go through the gates! Prepare the way of the people! Build up, build up the highway! Gather out the stones! Lift up a banner for the peoples.
11 Ubangiji ya yi shela ga iyakokin duniya cewa, “Faɗa wa Diyar Sihiyona, ‘Ga Mai Cetonki yana zuwa! Ga ladarsa tana tare da shi, sakamakonsa yana raka shi.’”
Behold, Yahweh has proclaimed to the end of the earth: “Say to the daughter of Zion, ‘Behold, your salvation comes! Behold, his reward is with him, and his recompense before him!’”
12 Za a ce da shi Tsattsarkar Mutane, Fansassu na Ubangiji; za a kuma ce da ke Wadda Aka Nema Birnin da Ba Za a Ƙara Yashe ta ba.
They will call them “The Holy People, Yahweh’s Redeemed”. You will be called “Sought Out, A City Not Forsaken”.

< Ishaya 62 >