< Ishaya 57 >

1 Mai adalci yakan mutu, ba kuwa wanda yakan yi tunani a zuciyarsa; an kwashe mutanen kirki, ba kuwa wanda ya fahimta cewa an kwashe masu adalci don a tsame su daga mugunta.
The righteous perish, but no one considers it, and the people of covenant faithfulness are gathered away, but no one understands that the righteous is gathered away from the evil.
2 Waɗanda suke aikata abin da yake daidai sukan shiga da salama; sukan huta yayinda suka kwanta cikin kabari.
He enters into peace; they rest in their beds, those who walk in their uprightness.
3 “Amma ku, ku matso nan, ku’ya’ya maza na masu sihiri, ku zuriyar mazinata da karuwai!
But come here, you sons of the sorceress, children of the adulterer and the woman who has prostituted herself.
4 Wane ne kuke yi wa ba’a? Ga wa kuke masa gwalo kuna kuma fitar da harshe? Ashe, ku ba tarin’yan tawaye ba ne, zuriyar maƙaryata?
Whom are you merrily mocking? Against whom are you opening the mouth and sticking out the tongue? Are you not children of rebellion, children of deceit?
5 Kuna cike da muguwar sha’awa mai ƙonawa a cikin itatuwan oak da kuma a ƙarƙashin kowane itace mai inuwa; kuna miƙa hadayar’ya’yanku a rafuffuka da kuma a ƙarƙashin tsagaggun duwatsu.
You heat yourselves up sleeping together under the oaks, under every green tree, you who kill your children in the dry riverbeds, under the rocky overhangs.
6 Gumakan da suke cikin duwatsu masu sulɓi su ne rabonku; su ɗin, su ne rabonku. I, gare su kuka kwarara hadayu na sha kuka kuma miƙa hadayu na gari. Saboda waɗannan abubuwa, zan yi haƙuri?
Among the smooth things of the river valley are the things that have been assigned to you. They are the object of your devotion. You pour out your drink offering to them and raise up a grain offering. In these things should I take pleasure?
7 Kun yi gadonku a dogayen duwatsu masu tsayi da kuma a tudu mai tsawo; a can kuka haura don ku miƙa hadayunku.
You prepared your bed on a high mountain; you also went up there to offer sacrifices.
8 A bayan ƙofofi da madogaran ƙofofi kuka kafa alamun gumakanku. Kuka yashe ni, kuka kware gadonku, kuka kwanta a kansa kuka fadada shi; kuka kuma ƙulla yarjejjeniya da waɗanda kuke ƙaunar gadajensu, kuka dubi tsiraicinsu.
Behind the door and the doorposts you set up your symbols; you deserted me, made yourselves naked, and went up; you made your bed wide. You made a covenant with them; you loved their beds; you saw their private parts.
9 Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol h7585)
You went to Molech with oil; you multiplied perfumes. You send your ambassadors far away; you went down to Sheol. (Sheol h7585)
10 Kuka gaji cikin dukan al’amuranku, amma ba ku iya cewa, ‘Aikin banza ne ba.’ Kuka sami sabuntar ƙarfinku, ta haka ba ku suma ba.
You were tired from your long journey, but you never said, “It is hopeless.” You found life in your hand; therefore you did not weaken.
11 “Wa ya sa ku fargaba, kuna jin tsoro har kuka yi mini ƙarya, ba ku kuma tuna da ni ba balle ku yi tunanin wannan a zukatanku? Ba don na daɗe ina shiru ba ne ya sa ba kwa tsorona?
“Whom are you worried about? Whom do you fear so much that has caused you to act so deceitfully, so much that you would not remember me or think about me? Because I was silent for so long, you are no longer afraid of me.
12 Zan bayyana adalcinku da kuma ayyukanku, ba kuwa za su amfane ku ba.
I will proclaim all your righteous acts and tell all that you have done, but they will not help you.
13 Sa’ad da kuka nemi taimako, bari tarin gumakanku su cece ku! Iska za tă kwashe dukansu tă tafi, ɗan numfashi kawai zai hura su. Amma mutumin da ya mai da ni mafakarsa zai gāji ƙasar ya kuma mallaki dutsena mai tsarki.”
When you cry out, let your collection of idols rescue you. Instead the wind will carry them all away, a breath will carry them all away. Yet he who takes refuge in me will inherit the land and will take possession of my holy mountain.
14 Za a kuma ce, “Ku gina, ku gina, ku gyara hanya! Ku kawar da abubuwan sa tuntuɓe a hanyar mutanena.”
He will say, 'Build, build! Clear a way! Remove all the stumbling blocks from the path of my people!'”
15 Gama abin da Maɗaukaki da kuma Mai daraja ya faɗa wanda yake raye har abada, wanda sunansa mai tsarki ne, “Ina zama a bisa da kuma a tsattsarkan wuri, amma kuma tare da shi wanda yake mai halin tuba mai tawali’u a ruhu, don in farfaɗo da ruhu mai tawali’u in kuma farfaɗo da zuciyar mai halin tuba.
For this is what the high and elevated One says, who lives eternally, whose name is holy, “I live in the exalted and holy place, with him also that is of a crushed and humble spirit, to revive the spirit of the humble ones, and to revive the heart of the contrite ones.
16 Ba zan tuhume su har abada ba, ba kuwa kullum zai yi fushi ba, gama a haka ruhun mutumin zan yi suma a gabana, shi numfashin mutumin da na halitta.
For I will not accuse forever, nor will I be angry forever, for then man's spirit would faint before me, the lives that I have made.
17 Na yi fushi saboda kwaɗayin zunubinsa; na yi masa horo, na kuma ɓoye fuskata saboda fushi, duk da haka ya ci gaba da ayyukan zunubinsa.
Because of the sin of his violent gain, I was angry, and I punished him; I hid my face and was angry, but he went backward in the way of his heart.
18 Na ga al’amuransa, amma zan warkar da shi; zan bi da shi in mayar da ta’aziyya a gare shi,
I have seen his ways, but I will heal him. I will lead him and comfort and console those who mourn for him,
19 ina ƙirƙiro yabo a leɓunan masu makoki a Isra’ila. Salama, salama, ga waɗanda suke nesa da kuma kusa,” in ji Ubangiji. “Zan kuma warkar da su.”
and I create the fruit of the lips. Peace, peace, to those who are far off and to those who are near—says Yahweh—I will heal them.
20 Amma mugaye suna kama da tumbatsar teku, wanda ba ya natsuwa, wanda raƙumansa sukan kawo gurɓacewa da tabo.
But the wicked are like the tossing sea, which cannot rest, and its waters churn up mire and mud.
21 “Babu salama ga mugaye,” in ji Allahna.
There is no peace for the wicked one—says God.”

< Ishaya 57 >