< Ishaya 53 >

1 Wa ya gaskata saƙonmu kuma ga wa hannun Ubangiji ya bayyana?
Któż uwierzył naszemu głoszeniu, a komu jest objawione ramię PANA?
2 Ya yi girma kamar dashe marar ƙarfi, kamar saiwa kuma daga ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da kyan gani ko wani makamin da zai ja hankalinmu, babu wani abin da yake da shi da zai sa mu yi sha’awarsa.
Wyrósł bowiem przed nim jak latorośl i jak korzeń z suchej ziemi. Nie miał kształtu ani urody; i gdy widzieliśmy go, nie było wyglądu, który by się nam podobał.
3 Mutane suka rena shi suka ƙi shi, mutum ne cike da baƙin ciki, ya kuma saba da wahala. Kamar wanda mutane suna ɓuya fuskokinsu daga gare shi aka rena shi aka yi banza da shi.
Wzgardzony i odrzucony przez ludzi; mąż boleści i doświadczony cierpieniem. I przed nim ukrywaliśmy jakby swoją twarz; wzgardzony tak, że mieliśmy go za nic.
4 Tabbatacce ya ɗauki cututtukanmu ya kuma daure da baƙin cikinmu duk da haka muka ɗauka Allah ya hukunta shi ne, ya buge shi ya kuma sa ya sha azaba.
Zaprawdę on wziął na siebie nasze cierpienia i nosił naszą boleść. A my uważaliśmy, że jest zraniony, uderzony przez Boga i utrapiony.
5 Amma aka yi masa rauni saboda laifofinmu, aka ƙuje shi saboda kurakuranmu; hukuncin da ya kawo mana salama ya kasance a kansa, kuma ta wurin mikinsa ya sa muka warke.
Lecz on był zraniony za nasze występki, starty za nasze nieprawości. Kara dla naszego pokoju była na nim, a jego ranami zostaliśmy uzdrowieni.
6 Dukanmu, muna kama da tumakin da suka ɓata, kowannenmu ya kama hanyarsa; Ubangiji kuwa ya sa hukunci ya auko a kansa hukuncin da ya wajaba a kanmu.
Wszyscy jak owce zbłądziliśmy, każdy z nas zboczył na swą drogę, a PAN włożył na niego nieprawość nas wszystkich.
7 Aka wulaƙanta shi aka kuma yi masa azaba, duk da haka bai buɗe bakinsa ba; aka kai shi kamar ɗan rago zuwa wurin yanka, kuma kamar tunkiya a gaban masu askinta tana shiru, haka bai buɗe bakinsa ba.
Uciśniony i gnębiony, ale nie otworzył swoich ust. Jak baranek na rzeź prowadzony i jak owca przed tymi, którzy ją strzygą, zamilkł i nie otworzył swoich ust.
8 Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.
Został zabrany z więzienia i z sądu. Kto wypowie jego pokolenie? Został bowiem wyrwany z ziemi żyjących i zraniony za przestępstwo mojego ludu.
9 Aka yi jana’izarsa tare da mugaye, aka binne shi tare da masu arziki, ko da yake bai taɓa yin wani tashin hankali ba, ko a sami ƙarya a bakinsa.
I wyznaczono mu grób z niegodziwcami, a z bogaczami była jego śmierć, choć nieprawości nie uczynił ani nie znaleziono fałszu w jego ustach.
10 Duk da haka nufin Ubangiji ne a ƙuje shi yă kuma sa yă sha wahala, kuma ko da yake Ubangiji ya sa ransa ya zama hadaya don zunubi, zai ga zuriyarsa zai kuma kawo masa tsawon rai, nufin Ubangiji kuma zai yi nasara a hannunsa.
Lecz spodobało się PANU zetrzeć go i zgnębić. A po złożeniu swojej duszy na ofiarę za grzech, ujrzy swoje potomstwo, przedłuży swoje dni i to, co się podoba PANU, przez jego rękę szczęśliwie się spełni.
11 Bayan wahalar ransa, zai ga hasken rai, ya kuma gamsu; ta wurin saninsa bawana mai adalci zai’yantar da mutane masu yawa, zai kuma ɗauki laifofinsu.
Z udręki swojej duszy ujrzy [owoc] i nasyci się. Mój sprawiedliwy sługa swoim poznaniem usprawiedliwi wielu, bo sam poniesie ich nieprawości.
12 Saboda haka zan ba shi rabo tare da manya, zai kuma raba ganima tare da masu ƙarfi, domin ya ba da ransa har mutuwa, aka kuma lissafta shi tare da masu laifofi. Gama ya ɗauki zunubin mutane masu yawa, ya kuma yi roƙo saboda laifofinsu.
Dlatego dam mu dział wśród wielkich, aby dzielił się zdobyczami z mocarzami, ponieważ wylał swoją duszę na śmierć. Został zaliczony do przestępców, sam poniósł grzech wielu i wstawił się za przestępcami.

< Ishaya 53 >