< Ishaya 48 >

1 “Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
Listen to this, descendants of Jacob, called by the name of Israel, and who come from the lineage of Judah. Listen, you people who swear by the name of the Lord, or who invoke the God of Israel, but not truly or sincerely.
2 ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
You say you're from the “Holy City,” and claim you're trusting in the God of Israel, whose name is the Lord Almighty.
3 na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
I predicted long ago what was going to happen—I said it and let people know. Then suddenly I decided to act, and it all came true.
4 Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
I know how stubborn you are, with necks as unbending as iron and foreheads as hard as bronze.
5 Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
I predicted these things to you long ago, before they happened. I explained them to you so that you couldn't say “My idol did this,” or “My image and my metal god ordered this to happen.”
6 Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
You've heard all I predicted, and seen it happen. Won't you admit it? Now I'm going to tell you new things, secrets you don't know anything about.
7 Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
These are brand-new, not something from the past. Before today you won't have heard anything about them, so you can't say, “Oh yes, I know about that.”
8 Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
No, you've never heard that, and you've never known that! Nobody's told you about that before! I know how deviously you operate—you're called “rebels from birth”!
9 Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
But because of my nature I am delaying my punishment; and because of my reputation, I'm not going to destroy you.
10 Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
Look how I've refined you, but not like silver—I chose you in the furnace of trouble.
11 Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
The reason I'm doing this is because of who I am, yes, because of my very nature. I won't let my reputation be damaged—I won't let anyone else have it.
12 “Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
Listen to me, Jacon, and Israel, the one I called. Only I am God. I am the first, and I am the last.
13 Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
I laid the foundations of the earth with my own hands; I personally spread out the heavens. When I call the stars, they all take their positions.
14 “Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
Everyone gather round and listen. Which of your “gods” told you anything like this? The one the Lord loves will carry out the Lord's wishes against Babylon—he will attack the Babylonians.
15 Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
I myself have spoken. I have called him to do this, and he will be successful in what he does.
16 “Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
Come close to me, and listen to this. From the very beginning I haven't spoken in secret; I am always there right when it happens. Now the Lord God and his Spirit has sent me to tell you this:
17 Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
This is what the Lord says, your Redeemer, the Holy One of Israel, I am the Lord your God. I am the one who teaches you what is good for you, who leads you along the way you should go.
18 Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
If you had only listened carefully to what I told you! Then your blessings would have flowed like a river, and goodness would have washed over you like the waves of the sea.
19 Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
Your children, your descendants, would have been like all those grains of sand. They wouldn't have had to be destroyed, wiped out before me.
20 Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
Leave Babylon! Run away from Babylonia with happy shouts! Let everyone know, telling the whole earth, “The Lord has redeemed his servant Jacob!”
21 Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
They weren't thirsty when he led them through the desert—he made water come out of the rock for them. He split the rock open and water poured out.
22 “Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.
The wicked have no peace, says the Lord.

< Ishaya 48 >