< Ishaya 28 >

1 Kaito ga wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim, ga fure mai yanƙwanewa, darajar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, ga birnin nan, wadda take girman kan waɗanda aka ƙasƙantar da ruwan inabinsu!
Malheur, couronne fastueuse des buveurs d’Ephraïm, diadème éphémère dont se pare son orgueil, qui entoure des têtes brillantes de parfums, étourdies par le vin!
2 Duba, Ubangiji yana da wanda yake da iko da kuma ƙarfi. Kamar dutsen ƙanƙara da kuma iska mai ɓarna, kamar kwararowar ruwa da rigyawa mai kirmewa, zai jefa shi har ƙasa da ƙarfi.
Voici venir, violent et impétueux, lancé par l’Eternel comme l’irruption de la grêle, un ouragan meurtrier; comme l’irruption de grandes eaux qui submergent tout, il le fait peser sur le sol avec puissance.
3 Za a tattaka wannan rawani, girman kai na mashayan Efraim da ƙafa.
Elle sera foulée aux pieds, la couronne fastueuse des buveurs d’Ephraïm,
4 Wannan fure mai yanƙwanewa, darajarar kyansa, da aka sa a kan kwari mai ba da amfani, zai zama kamar’ya’yan ɓaure, nunan fari, da zarar wani ya gani ya kuma tsinka, zai haɗiye shi.
et il adviendra de ce diadème flétri qui pare son orgueil, qui couronne sa tête brillante de parfums, comme d’une primeur avant l’été, laquelle, à peine aperçue, à peine dans la main, est déjà dévorée.
5 A wannan rana Ubangiji Maɗaukaki zai zama rawani mai daraja kyakkyawan rawani wa mutanensa da suka ragu.
En ce jour, l’Eternel-Cebaot sera une couronne de gloire et un splendide diadème pour le reste de son peuple,
6 Zai zama ruhun adalci gare shi wanda yake zaune a kujerar shari’a, wurin samun ƙarfi ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofi.
et une inspiration de justice à ceux qui siègent pour la justice, de courage à ceux qui repoussent les attaques près des portes.
7 Da waɗannan kuma masu tangaɗi saboda sun sha ruwan inabi suke jiri don sun sha barasa Firistoci da annabawa suna tangaɗi saboda sun sha barasa sun kuma yi tatur da ruwan inabi; suna jiri saboda sun sha barasa, suna tangaɗi sa’ad da suke ganin wahayi, suna tuntuɓe sa’ad da suke ba da shawara.
Toutefois, eux aussi sont troublés par le vin, égarés par la boisson; prêtre et prophète trébuchent à cause de la boisson, sont étourdis par le vin, pris de vertige par suite d’ivresse; leur vision est devenue trouble et ils vacillent dans leurs jugements.
8 Duk amai ya rufe teburori kuma babu wani wurin da ba a ɓata ba.
En effet, toutes les tables sont couvertes de vomissures et d’immondices; pas un coin n’y échappe.
9 “Wane ne yake so ya koyar? Ga wa yake bayyana saƙonsa? Ga yaran da aka yaye, ga waɗanda ba a daɗe da yayewa ba ne?
"À qui donc veut-il enseigner la science? À qui inculquer des leçons? À des enfants qui viennent d’être sevrés, de quitter la mamelle.
10 Gama haka yake. Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki a kan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan.”
Ce n’est que loi sur loi, précepte sur précepte, règle sur règle, ordre sur ordre, une vétille par ci, une vétille par là!"
11 To da kyau, da leɓunan baƙi da ku harsunan da ba sani ba Allah zai yi magana da wannan mutane,
Sans doute c’est dans une langue barbare et dans un idiome étranger qu’il parlait à ce peuple,
12 waɗanda zai ce, “Wannan shi ne wurin hutu, bari waɗanda suka gaji su huta”; da kuma, “Wannan shi ne wurin wartsakewa” amma sun ƙi su saurara.
lorsqu’il leur disait: "Ceci est la paix donnez du relâche à ceux qui sont Ias ceci est le repos!" Ils n’ont pas voulu écouter.
13 Saboda haka fa, maganar Ubangiji gare su za tă zama, Yi ka kuma yi, yi ka kuma yi, mulki akan mulki, mulki a kan mulki; nan kaɗan, can kaɗan, domin su tafi su kuma fāɗi da baya, su ji rauni a kuma kama su da tarko, a kai su zaman bauta.
Ils n’ont vu dans la parole du Seigneur que loi sur loi, précepte sur précepte, règle sur règle, ordre sur ordre, une vétille par ci, une vétille par là, de sorte qu’en marchant ils trébuchent en arrière et se brisent, s’engagent dans le piège et s’y embarrassent.
14 Saboda haka ku saurari maganar Ubangiji, ku masu ba’a ku da kuke mulkin wannan mutane a Urushalima.
En vérité, écoutez la parole de l’Eternel, ô gens de raillerie, vous qui dominez ce peuple dans Jérusalem.
15 Kuna fariya cewa, “Mun yi alkawari da mutuwa, mun kuma yi yarjejjeniya da kabari. Sa’ad da zafi ya ratsa, ba zai taɓa mu ba, gama mun mai da ƙarya mafakarmu ruɗu kuma wurin ɓuyanmu.” (Sheol h7585)
Vous avez dit: "Nous avons contracté une alliance—avec la mort, conclu un pacte avec le Cheol; lorsque passera le fléau dévastateur, il ne nous atteindra pas, car nous avons fait de la fraude notre abri et du mensonge notre refuge." (Sheol h7585)
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
Mais ainsi a parlé le Seigneur, l’Eternel: Voici, je vais, dans Sion, ériger une pierre de fondation, une pierre éprouvée, une précieuse pierre d’angle solidement fixée; quiconque s’y appuiera ne sera pas réduit à fuir.
17 Zan mai da gaskiya igiyar gwaji adalci kuma ɗan katakon gwajin ginin; ƙanƙara za tă share mafakarku, ƙarya, da ruwa kuma za su mamaye maɓuyanku.
J’Emploierai le droit comme cordeau et la justice comme fil à plomb; la grêle balayera l’abri de la fraude et les eaux entraîneront son refuge.
18 Za a soke alkawarinku da mutuwa; yarjejjeniyarku da kabari ba zai zaunu ba. Sa’ad da zafi mai ɓarna ya ratsa, zai hallaka ku. (Sheol h7585)
Alors sera rompue votre alliance avec la mort, votre pacte avec le Cheol ne tiendra pas: lorsque s’avancera le fléau dévastateur, vous en serez écrasés. (Sheol h7585)
19 A duk sa’ad da ya zo; ko da safiya, ko dare ko kuma da rana, zai yi ta ratsawa yana kwasanku.” Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana,
Toutes les fois qu’il passera, il vous emportera; matin après matin il passera, le jour et la nuit, et rien que d’en percevoir le bruit sera un sujet d’épouvante.
20 wanda ya yi ƙoƙari yă kwanta a gajeren gado, yă kuma rufa da ɗan siririn bargo.
Trop courte sera la couche pour s’y étendre, et trop étroite la couverture pour s’y envelopper.
21 Ubangiji zai tashi kamar yadda ya yi a Dutsen Feratsim, zai tā da kansa kamar a Kwarin Gibeyon don yă aikata aikinsa, aikinsa da ba a saba gani ba, yă kuma yi aikinsa, baƙon aikinsa.
Car l’Eternel se lèvera comme sur la montagne de Peracim, et il manifestera sa colère comme dans la vallée de Gabaon, pour accomplir son œuvre étrange est son œuvre, et pour exécuter son labeur extraordinaire est son labeur.
22 Yanzu ku daina ba’arku, in ba haka ba sarƙoƙinku za su ƙara nauyi; Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa mini game da hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasar.
Maintenant donc, trêve à vos railleries! Elles renforceraient vos chaînes; car c’est un arrêt de destruction que j’ai entendu prononcer par le Seigneur, l’Eternel-Cebaot, contre tout le pays.
23 Ku saurara ku kuma ji muryata; ku kasa kunne ku kuma ji abin da na faɗa.
Prêtez l’oreille et écoutez ma voix, soyez attentifs et entendez mon discours.
24 Sa’ad da manomi ya yi noma don shuki, yakan ci gaba da noma ne? Yakan ci gaba da sara yana yin kunyoyi a ƙasa ne?
Le laboureur passe-t-il tout son temps à labourer en vue de semer? À fendre le sol et à promener la herse dans son champ?
25 Sa’ad da ya shirya wuri da kyau, ba yakan shuka kanumfari ya kuma yayyafa ɗaɗɗoya ba? Ba yakan shuka alkama a kunyoyinsa sha’ir a kunyoyinsa, tamba kuma a filinsa ba?
N’Est-ce pas? Quand il en a égalisé la surface, il y répand de la vesce, y jette du cumin, sème le froment dans les sillons, l’orge aux endroits désignés et l’épeautre sur les bords.
26 Allahnsa ya umarce shi ya kuma koya masa hanyar da take daidai.
C’Est son Dieu qui lui a enseigné la règle à suivre, c’est lui qui l’a instruit.
27 Ba a bugan kanumfari da ƙaton sanda ko a yi ta jujjuye ƙafar keke a kan ɗaɗɗoya; akan buga kanumfari da siririn sanda ɗaɗɗoya kuma da tsumagiya.
De même ce n’est pas avec le rouleau tranchant que la vesce est battue, ce n’est pas la roue du chariot qu’on fait passer sur le cumin: la vesce est battue avec le bâton et le cumin avec la verge.
28 Dole a niƙa hatsi don a yi burodi; saboda haka mutum ba zai yi ta bugun alkama, har yă ɓata tsabar ba. Ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba.
Mais le blé dont on fait le pain doit être écrasé; il ne sert de rien de le battre indéfiniment, d’y faire passer avec force les roues du chariot et les chevaux, ce qui ne le réduit pas en poussière.
29 Dukan wannan hikimar takan zo daga Ubangiji Maɗaukaki ne, shi da yake mashawarci mai banmamaki, mafifici kuma cikin hikima.
Cela aussi émane de l’Eternel-Cebaot: il conçoit des desseins merveilleux et déploie une haute sagesse.

< Ishaya 28 >