< Hosiya 11 >

1 “Sa’ad da Isra’ila yake yaro, na ƙaunace shi, daga Masar kuma na kira ɗana.
هنگامی که اسرائیل طفل بود او رادوست داشتم و پسر خود را از مصرخواندم.۱
2 Amma yawan kiran da na yi wa Isra’ila haka nesa da ni da suke ta yi. Suka miƙa hadaya ga Ba’al suka kuma ƙona turare ga siffofi.
هر قدر که ایشان را بیشتر دعوت کردند، بیشتر از ایشان دور رفتند و برای بعلیم قربانی گذرانیدند و به جهت بتهای تراشیده بخورسوزانیدند.۲
3 Ni ne na koya wa Efraim tafiya ina kama su da hannu; amma ba su gane cewa ni ne na warkar da su ba.
و من راه رفتن را به افرایم تعلیم دادم و او را به بازوها برداشتم، اما ایشان ندانستند که من ایشان را شفا داده‌ام.۳
4 Na bishe su da linzamin alheri da tausayi, da ragamar ƙauna; Na cire karkiya daga wuyansu na kuma rusuna na ciyar da su.
ایشان را به ریسمانهای انسان و به بندهای محبت جذب نمودم و به جهت ایشان مثل کسانی بودم که یوغ را از گردن ایشان برمی دارند و خوراک پیش روی ایشان نهادم.۴
5 “Ba za su koma Masar ba Assuriya kuma ba za tă yi mulki a bisansu ba saboda sun ƙi su tuba ba?
به زمین مصر نخواهد برگشت، اما آشورپادشاه ایشان خواهد شد چونکه از بازگشت نمودن ابا کردند.۵
6 Takuba za su yi ta wulgawa a biranensu, za su hallaka sandunan ƙarafan ƙofofinsu su kuma kawo ƙarshen ƙulle-ƙullensu.
شمشیر بر شهرهایش هجوم خواهد آورد و پشت بندهایش را به‌سبب مشورت های ایشان معدوم و نابود خواهدساخت.۶
7 Mutanena sun ƙudura su juye daga gare ni. Ko da ma suka yi kira ga Mafi Ɗaukaka, ta ko ƙaƙa ba zai girmama su ba.
و قوم من جازم شدند که از من مرتدگردند. و هر‌چند ایشان را بسوی حضرت اعلی دعوت نمایند لکن کسی خویشتن رابرنمی افرازد.۷
8 “Yaya zan ba da kai, Efraim? Yaya zan miƙa ka, Isra’ila? Yaya zan yi da kai kamar Adma? Yaya zan yi da kai kamar Zeboyim? Zuciyata ta canja a cikina; dukan tausayina ya huru.
‌ای افرایم چگونه تو را ترک کنم و‌ای اسرائیل چگونه تو را تسلیم نمایم؟ چگونه تو رامثل ادمه نمایم و تو را مثل صبوئیم سازم؟ دل من در اندرونم منقلب شده و رقت های من با هم مشتعل شده است.۸
9 Ba zan zartar da fushina mai zafi ba, ba kuwa zan juya in ragargaza Efraim ba. Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Mai Tsarki a cikinku. Ba zan zo cikin fushi ba.
حدت خشم خود را جاری نخواهم ساخت و بار دیگر افرایم را هلاک نخواهم نمود زیرا خدا هستم وانسان نی و درمیان تو قدوس هستم، پس به غضب نخواهم آمد.۹
10 Za su bi Ubangiji; zai yi ruri kamar zaki. Sa’ad da ya yi ruri,’ya’yansa za su zo da rawan jiki daga yamma.
ایشان خداوند را پیروی خواهند نمود. اومثل شیر غرش خواهد نمود و چون غرش نماید فرزندان از مغرب به لرزه خواهند آمد.۱۰
11 Za su zo da rawan jiki kamar tsuntsaye daga Masar, kamar kurciyoyi daga Assuriya. Zan zaunar da su a cikin gidajensu,” in ji Ubangiji.
مثل مرغان از مصر و مانند کبوتران از زمین آشور لرزان خواهند آمد. خداوند می‌گوید که ایشان را در خانه های ایشان ساکن خواهم گردانید.۱۱
12 Mutanen Efraim sun kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra’ila da ruɗu. Mutanen Yahuda kuma suna yi wa Allah ƙin ji, har ma a kan Mai Tsarkin nan mai aminci.
افرایم مرا به دروغها و خاندان اسرائیل به مکرها احاطه کرده‌اند و یهودا هنوز با خدا و باقدوس امین ناپایدار است.۱۲

< Hosiya 11 >