< Habakkuk 3 >

1 Addu’ar annabi Habakkuk. A kan shigiyont.
A prayer of Habakkuk, the prophet, set to victorious music.
2 Ya Ubangiji, na ji irin shaharar da ka yi; na yi al’ajabi game da ayyukanka, ya Ubangiji. Ka maimaita su a kwanakinmu, ka sanar da su a lokacinmu; ka yi jinƙai ko a lokacin da kake fushi.
Yahweh, I have heard of your fame. I stand in awe of your deeds, Yahweh. Renew your work in the middle of the years. In the middle of the years make it known. In wrath, you remember mercy.
3 Allah ya zo daga Teman, Mai Tsarkin nan daga Dutsen Faran. (Sela) Ɗaukakarsa ta rufe sammai yabonsa kuma ya cika duniya.
God came from Teman, the Holy One from Mount Paran. (Selah) His glory covered the heavens, and his praise filled the earth.
4 Darajarsa ta yi kamar fitowar rana; ƙyalƙyali ya wulga daga hannunsa, inda ikonsa yake a ɓoye.
His splendor is like the sunrise. Rays shine from his hand, where his power is hidden.
5 Annoba ta sha gabansa; cuta kuma tana bin bayansa.
Plague went before him, and pestilence followed his feet.
6 Ya tsaya, ya kuwa girgiza duniya; ya duba, sai ya sa al’ummai suka yi rawan jiki. Tsofaffin duwatsu sun wargaje daɗaɗɗun tuddai kuma suka rurrushe. Hanyoyinsa dawwammamu ne.
He stood, and shook the earth. He looked, and made the nations tremble. The ancient mountains were crumbled. The age-old hills collapsed. His ways are eternal.
7 Na ga tentin Kushan cikin azaba; wuraren zaman Midiyan cikin damuwa.
I saw the tents of Cushan in affliction. The dwellings of the land of Midian trembled.
8 Ka ji haushin koguna ne, ya Ubangiji? Ko kuwa ka hasala da rafuffuka ne? Ko ka yi fushi da teku ne sa’ad da ka hau dawakanka da kuma kekunan yaƙinka masu nasara?
Was Yahweh displeased with the rivers? Was your anger against the rivers, or your wrath against the sea, that you rode on your horses, on your chariots of salvation?
9 Ka ja bakanka, ka nemi a ba ka kibiyoyi masu yawa. (Sela) Ka raba duniya da koguna;
You uncovered your bow. You called for your sworn arrows. (Selah) You split the earth with rivers.
10 duwatsu sun gan ka sai suka ƙame. Ruwaye masu hauka sun yi ta fantsamawa; zurfafa suka yi ruri suka tā da raƙuman ruwansu sama.
The mountains saw you, and were afraid. The storm of waters passed by. The deep roared and lifted up its hands on high.
11 Rana da wata suka tsaya cik a sammai da ganin kibiyoyinka masu wucewa fyu, da ganin hasken māshinka mai walƙiya.
The sun and moon stood still in the sky at the light of your arrows as they went, at the shining of your glittering spear.
12 Cikin hasala ka ratsa duniya cikin fushi kuma ka tattake ƙasashe.
You marched through the land in wrath. You threshed the nations in anger.
13 Ka fito don ka fanshi mutanenka, don ceci shafaffenka. Ka ragargaza shugaban ƙasar mugaye, ka tuɓe shi daga kai har ƙafa. (Sela)
You went out for the salvation of your people, for the salvation of your anointed. You crushed the head of the land of wickedness. You stripped them head to foot. (Selah)
14 Da māshinsa ka soki kansa sa’ad da jarumawansa suka fito don su tarwatse mu, suna farin ciki sai ka ce masu shirin cinye matalautan da suke a ɓoye.
You pierced the heads of his warriors with their own spears. They came as a whirlwind to scatter me, gloating as if to devour the wretched in secret.
15 Ka tattake teku da dawakanka, kana kaɗa manyan ruwaye.
You trampled the sea with your horses, churning mighty waters.
16 Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
I heard, and my body trembled. My lips quivered at the voice. Rottenness enters into my bones, and I tremble in my place because I must wait quietly for the day of trouble, for the coming up of the people who invade us.
17 Ko da yake itace ɓaure bai tohu ba, ba kuma’ya’ya a kuringar inabi, ko da yake zaitun bai ba da amfani ba, gonaki kuma ba su ba da abinci ba, ko da yake babu tumaki a garke, ba kuma shanu a turaku,
For even though the fig tree doesn’t flourish, nor fruit be in the vines, the labor of the olive fails, the fields yield no food, the flocks are cut off from the fold, and there is no herd in the stalls,
18 duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, zan yi murna da Allah Mai Cetona.
yet I will rejoice in Yahweh. I will be joyful in the God of my salvation!
19 Ubangiji Mai Iko Duka shi ne ƙarfina; yakan mai da ƙafafuna kamar na barewa, yakan sa in yi tafiya a wurare masu tsayi.
Yahweh, the Lord, is my strength. He makes my feet like deer’s feet, and enables me to go in high places. For the music director, on my stringed instruments.

< Habakkuk 3 >