< Habakkuk 1 >

1 Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
Пророцтво, яке бачив пророк Аваку́м.
2 Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
Аж до́ки я, Господи, кли́кати буду, а Ти не почуєш? До тебе я кли́чу: „Наси́льство!“та Ти не спаса́єш!
3 Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
Для чого непра́вість мені Ти показуєш та позира́єш на му́ку? А передо мною грабі́ж та наси́льство, і супере́чка стається, і но́ситься сва́рка.
4 Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
Тому то Зако́н припиня́ється, і не виходить до чину наза́всіди право, бо несправедливий вигу́блює праведного, тому правосуддя вихо́дить покри́вленим.
5 “Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
Пригля́ньтеся ви до наро́дів, і диві́ться, і ду́же здиву́йтесь, бо вчиню́ Я за ваших днів ді́ло, про яке не повірите ви, коли буде розка́зане.
6 Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
Бо оце Я поставлю халде́їв, народ лютий та скорий, що ґрасу́є по широкій землі, щоб захопи́ти оселі, які не його.
7 Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
Страшни́й та грізни́й він, — від нього само́го вихо́дить і право його, і вели́кість його.
8 Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
І від панте́р його коні швидші, і від вовкі́в вечеро́вих люті́ші. І розлетя́ться його́ верхівці́, а їздці́ його зда́лека при́йдуть, — вони будуть леті́ти, нена́че орел, що на їжу поспіша́є.
9 duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
Він прихо́дить увесь на наси́льство, а ціль їх обличчя — вперед, і набере́ полоне́них, як то́го піску́.
10 Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
І він глузу́є з царів, а князі́ — сміх для нього. Він сміється з тверди́ні усякої, бо на вал насипа́є землі, і її здобува́є!
11 Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
Тоді він несеться, як вітер, і пере́йде, і згріши́ть, бо зро́бить за бога свого́ оцю силу свою́.
12 Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
Хіба ж Ти не відда́вна, о Господи? Боже Ти мій, мій Святий, — не помре́мо! Господи, Ти для суду поставив його́, і, о Скеле, призначив його на кара́ння!
13 Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
Твої очі зана́дто пречисті, щоб міг Ти дивитись на зло, і на наси́льство дивитись не можеш. Чому ж дивишся Ти на грабі́жників, мовчиш, коли несправедливий винищує справедливішого від се́бе?
14 Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
Ти ж маєш людей, як у морі тих риб, немов ту черву́, що пана над нею нема.
15 Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
Усе́ це грабіжник витя́гує ву́дкою, своїм не́водом тя́гне оце́, та збирає оце́ в свою сітку, тому ті́шиться він та радіє.
16 Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
Тому жертву прино́сить він не́водові, — і ка́дить для сітки своєї, бо від них ситий у́діл його та добі́рна пожи́ва його!
17 Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?
Чи на це випоро́жнює він свого не́вода, і за́вжди гото́в убивати наро́ди без милости?

< Habakkuk 1 >