< Farawa 15 >

1 Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
After these things the word of the LORD came unto Abram in a vision, saying: 'Fear not, Abram, I am thy shield, thy reward shall be exceeding great.'
2 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
And Abram said: 'O Lord GOD, what wilt Thou give me, seeing I go hence childless, and he that shall be possessor of my house is Eliezer of Damascus?'
3 Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
And Abram said: 'Behold, to me Thou hast given no seed, and, lo, one born in my house is to be mine heir.'
4 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
And, behold, the word of the LORD came unto him, saying: 'This man shall not be thine heir; but he that shall come forth out of thine own bowels shall be thine heir.'
5 Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
And He brought him forth abroad, and said: 'Look now toward heaven, and count the stars, if thou be able to count them'; and He said unto him: 'So shall thy seed be.'
6 Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
And he believed in the LORD; and He counted it to him for righteousness.
7 Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
And He said unto him: 'I am the LORD that brought thee out of Ur of the Chaldees, to give thee this land to inherit it.'
8 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
And he said: 'O Lord GOD, whereby shall I know that I shall inherit it?'
9 Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
And He said unto him: 'Take Me a heifer of three years old, and a she-goat of three years old, and a ram of three years old, and a turtle-dove, and a young pigeon.'
10 Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
And he took him all these, and divided them in the midst, and laid each half over against the other; but the birds divided he not.
11 Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
And the birds of prey came down upon the carcasses, and Abram drove them away.
12 Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
And it came to pass, that, when the sun was going down, a deep sleep fell upon Abram; and, lo, a dread, even a great darkness, fell upon him.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
And He said unto Abram: 'Know of a surety that thy seed shall be a stranger in a land that is not theirs, and shall serve them; and they shall afflict them four hundred years;
14 Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
and also that nation, whom they shall serve, will I judge; and afterward shall they come out with great substance.
15 Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
But thou shalt go to thy fathers in peace; thou shalt be buried in a good old age.
16 A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
And in the fourth generation they shall come back hither; for the iniquity of the Amorite is not yet full.'
17 Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
And it came to pass, that, when the sun went down, and there was thick darkness, behold a smoking furnace, and a flaming torch that passed between these pieces.
18 A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
In that day the LORD made a covenant with Abram, saying: 'Unto thy seed have I given this land, from the river of Egypt unto the great river, the river Euphrates;
19 ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
the Kenite, and the Kenizzite, and the Kadmonite,
20 Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
and the Hittite, and the Perizzite, and the Rephaim,
21 Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”
and the Amorite, and the Canaanite, and the Girgashite, and the Jebusite.'

< Farawa 15 >