< Farawa 15 >

1 Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
After these things, the worde of the Lord came vnto Abram in a vision, saying, Feare not, Abram, I am thy buckler, and thine exceeding great reward.
2 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
And Abram said, O Lord God, what wilt thou giue me, seeing I goe childlesse, and the steward of mine house is this Eliezer of Damascus?
3 Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
Againe Abram saide, Beholde, to me thou hast giuen no seede: wherefore loe, a seruant of mine house shalbe mine heire.
4 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
Then beholde, the worde of the Lord came vnto him, saying, This man shall not be thine heire, but one that shall come out of thine owne bowels, he shalbe thine heire.
5 Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
Moreouer he brought him forth and said, Looke vp nowe vnto heauen, and tell ye starres, if thou be able to number them: and he said vnto him, So shall thy seede be.
6 Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
And Abram beleeued the Lord, and he counted that to him for righteousnesse.
7 Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
Againe he saide vnto him, I am the Lord, that brought thee out of Vr of the Caldees, to giue thee this land to inherite it.
8 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
And he said, O Lord God, whereby shall I knowe that I shall inherite it?
9 Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
Then he said vnto him, Take me an heifer of three yeeres olde, and a shee goate of three yeeres olde, and a ramme of three yeeres olde, a turtle doue also and a pigeon.
10 Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
So he tooke all these vnto him, and deuided them into the middes, and laid euery piece one against an other: but the birdes deuided he not.
11 Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
Then foules fell on the carkases, and Abram droue them away.
12 Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
And when the sunne went downe, there fell an heauie sleepe vpon Abram: and loe, a very fearefull darkenes fell vpon him.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
Then he saide to Abram, Knowe for a suretie, that thy seede shalbe a stranger in a land, that is not theirs, foure hundreth yeeres, and shall serue them: and they shall intreate them euill.
14 Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
Notwithstanding the nation, whom they shall serue, will I iudge: and afterward shall they come out with great substance.
15 Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
But thou shalt goe vnto thy fathers in peace, and shalt be buried in a good age.
16 A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
And in the fourth generation they shall come hither againe: for the wickednes of the Amorites is not yet full.
17 Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
Also when the sunne went downe, there was a darkenes: and behold, a smoking fornace, and a firebrand, which went betweene those pieces.
18 A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
In that same day the Lord made a couenant with Abram, saying, Vnto thy seede haue I giuen this lande, from the riuer of Egypt vnto the great riuer, the riuer Euphrates.
19 ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
The Kenites, and the Kenizites, and the Kadmonites,
20 Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
And the Hittites, and the Perizzites, and the Rephaims,
21 Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”
The Amorites also, and the Canaanites, and the Girgashites, and the Iebusites.

< Farawa 15 >