< Farawa 15 >

1 Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
And after these things the word of the Lord came to Abram in a vision, saying, Fear not, Abram, I shield you, your reward shall be very great.
2 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
And Abram said, Master [and] Lord, what will you give me? whereas I am departing without a child, but the son of Masek my home-born female slave, this Eliezer of Damascus [is mine heir.]
3 Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
And Abram said, [I am grieved] since you have given me no seed, but my home-born [servant] shall succeed me.
4 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
And immediately there was a voice of the Lord to him, saying, This shall not be your heir; but he that shall come out of you shall be your heir.
5 Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
And he brought him out and said to him, Look up now to heaven, and count the stars, if you shall be able to number them fully, and he said, Thus shall your seed be.
6 Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
And Abram believed God, and it was counted to him for righteousness.
7 Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
And he said to him, I am God that brought you out of the land of the Chaldeans, so as to give you this land to inherit.
8 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
And he said, Master [and] Lord, how shall I know that I shall inherit it?
9 Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
And he said to him, Take for me an heifer in her third year, and a she-goat in her third year, and a ram in his third year, and a dove and a pigeon.
10 Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
So he took to him all these, and divided them in the midst, and set them opposite to each other, but the birds he did not divide.
11 Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
And birds came down upon the bodies, [even] upon the divided parts of them, and Abram sat down by them.
12 Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
And about sunset a trance fell upon Abram, and behold! a great gloomy terror falls upon him.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
And it was said to Abram, You shall surely know that your seed shall be a sojourner in a land not their won, and they shall enslave them, and afflict them, and humble them four hundred years.
14 Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
And the nation whoever they shall serve I will judge; and after this, they shall come forth hither with much property.
15 Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
But you shall depart to your fathers in peace, nourished in a good old age.
16 A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
And in the fourth generation they shall return hither, for the sins of the Amorites are not yet filled up, even until now.
17 Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
And when the sun was about to set, there was a flame, and behold a smoking furnace and lamps of fire, which passed between these divided pieces.
18 A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
In that day the Lord made a covenant with Abram, saying, To your seed I will give this land, from the river of Egypt to the great river Euphrates.
19 ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
The Kenites, and the Kenezites, and the Kedmoneans,
20 Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
and the Chettites, and the Pherezites, and the Raphaim,
21 Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”
and the Amorites, and the Chananites, and the Evites, and the Gergesites, and the Jebusites.

< Farawa 15 >