< Ezra 10 >

1 Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
As Ezra prayed and confessed, he wept and threw himself down before God's house. A very great assembly of Israelite men, women, and children gathered to him, for the people were weeping very greatly.
2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
Shekaniah son of Jehiel of the descendants of Elam said to Ezra, “We have been unfaithful to our God and have married foreign women from the people of the other lands. But in spite of this, there is still hope for Israel.
3 Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
So now let us make a covenant with our God to send out all the women and their children according to the Lord's instructions and the instructions of those who tremble at the commandments of our God, and let it be done according to the law.
4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
Arise, for this thing is for you to carry out, and we are with you. Be strong and do this.”
5 Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
So Ezra rose and made the priestly officials, the Levites, and all of Israel promise to act in this way. So they all took a solemn oath.
6 Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
Then Ezra rose from before God's house and went to the rooms of Jehohanan son of Eliashib. He did not eat any bread or drink any water, since he was mourning concerning the faithlessness of those who had been in captivity.
7 Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
So they sent word in Judah and Jerusalem to all the people back from exile to assemble in Jerusalem.
8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
Anyone who did not come in three days according to the instructions from the officials and elders forfeited all of his possessions and would be excluded from the great assembly of the people who had come back from exile.
9 A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
So all the men of Judah and Benjamin assembled in Jerusalem in three days. It was the ninth month and the twentieth day of the month. All the people stood in the square before God's house and trembled because of the word and the rain.
10 Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
Ezra the priest arose and said, “You yourselves have committed treason. You lived with foreign women so as to increase Israel's guilt.
11 Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
But now give praise to Yahweh, your ancestors' God, and do his will. Separate from the people of the land and from the foreign women.”
12 Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
All the assembly answered in a loud voice, “We will do as you have said.
13 Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
However, there are many people, and it is the rainy season. We have no strength to stand outside, and this is not only one or two days of work, since we have greatly transgressed in this matter.
14 Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
So let our officials represent all the assembly. Let all who have allowed foreign women to live in our cities come at the time that will be fixed with the city elders and the city judges until the raging wrath of our God goes away from us.”
15 Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
Jonathan son of Asahel and Jahzeiah son of Tikvah opposed this, and Meshullam and Shabbethai the Levite supported them.
16 Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
So the people who returned from exile did this. Ezra the priest selected men, the leaders in their ancestors' clans and houses—all of them by name, and they looked into the matter on the first day of the tenth month.
17 A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
By the first day of the first month they had finished discovering which men had lived with foreign women.
18 A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
Among the descendants of the priests there were those who had lived with foreign women. Among the descendants of Jeshua son of Jozadak and his brothers there were Maaseiah, Eliezer, Jarib, and Gedaliah.
19 (Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
So they determined to send their wives away. Since they were guilty, they offered a ram from the flock for their guilt.
20 Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
Among the descendants of Immer: Hanani and Zebadiah.
21 Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
Among the descendants of Harim: Maaseiah, Elijah, Shemaiah, Jehiel, and Uzziah.
22 Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
Among the descendants of Pashhur: Elioenai, Maaseiah, Ishmael, Nethanel, Jozabad, and Elasah.
23 Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
Among the Levites: Jozabad, Shimei, Kelaiah—that is, Kelita, Pethahiah, Judah, and Eliezer.
24 Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
Among the singers: Eliashib. Among the gatekeepers: Shallum, Telem, and Uri.
25 Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
Among the rest of the Israelites—among the descendants of Parosh: Ramiah, Izziah, Malchijah, Mijamin, Eleazar, Malchijah, and Benaiah.
26 Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
Among the descendants of Elam: Mattaniah, Zechariah, Jehiel, Abdi, Jeremoth, and Elijah.
27 Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
Among the descendants of Zattu: Elioenai, Eliashib, Mattaniah, Jeremoth, Zabad, and Aziza.
28 Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
Among the descendants of Bebai: Jehohanan, Hananiah, Zabbai, and Athlai.
29 Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
Among the descendants of Bani: Meshullam, Malluk, Adaiah, Jashub, and Sheal Jeremoth.
30 Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
Among the descendants of Pahath-Moab: Adna, Kelal, Benaiah, Maaseiah, Mattaniah, Bezalel, Binnui, and Manasseh.
31 Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
Among the descendants of Harim: Eliezer, Ishijah, Malchijah, Shemaiah, Shimeon,
32 Benyamin, Malluk da Shemariya.
Benjamin, Malluk, and Shemariah.
33 Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
Among the descendants of Hashum: Mattenai, Mattattah, Zabad, Eliphelet, Jeremai, Manasseh, and Shimei.
34 Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
Among the descendants of Bani: Maadai, Amram, Uel,
35 Benahiya, Bedeya, Keluhi,
Benaiah, Bedeiah, Keluhi,
36 Baniya, Meremot, Eliyashib,
Vaniah, Meremoth, Eliashib,
37 Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
Mattaniah, Mattenai, and Jaasu.
38 Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
Among the descendants of Binnui: Shimei,
39 Shelemiya, Natan, Adahiya,
Shelemiah, Nathan, Adaiah,
40 Maknadebai, Shashai, Sharai,
Maknadebai, Shashai, Sharai,
41 Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
Azarel, Shelemiah, Shemariah,
42 Shallum da Amariya da Yusuf.
Shallum, Amariah, and Joseph.
43 Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
Among the descendants of Nebo: Jeiel, Mattithiah, Zabad, Zebina, Jaddai, Joel, and Benaiah.
44 Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.
All of these had taken foreign wives and had children with some of them.

< Ezra 10 >