< Ezekiyel 47 >

1 Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
Adam beni tapınağın girişine geri getirdi. Doğuya doğru tapınağın kapı eşiğinin altından sular aktığını gördüm. Tapınak doğuya bakıyordu. Sular tapınağın güney yanının altından, sunağın güneyinden aşağıya akıyordu.
2 Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
Beni oradan, Kuzey Kapısı'ndan çıkarıp dış yoldan doğuya bakan dış kapıya götürdü. Sular güney yönünden akıyordu.
3 Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
Adam elinde bir ölçü ipiyle doğuya doğru gitti. Bin arşın ölçtükten sonra beni ayak bileğine dek çıkan sulara getirdi.
4 Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
Bin arşın daha ölçtü ve beni dize kadar çıkan sulara getirdi. Bin arşın daha ölçtü, beni bele kadar çıkan sulara getirdi.
5 Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
Bin arşın daha ölçtü, içinden geçemediğim bir ırmak oluştu. Sular yükselmişti, içinden yürüyerek karşıya geçilemezdi, yüzülecek kadar derin bir ırmak oluşmuştu.
6 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
Bana, “İnsanoğlu, bunu gördün mü?” diye sordu. Daha sonra beni ırmağın kıyısına geri getirdi.
7 Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
Oraya varınca, ırmağın her iki kıyısında birçok ağaç gördüm.
8 Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
Bana şöyle dedi: “Bu sular doğu bölgesine doğru akıyor, oradan Arava Vadisi'ne, sonra Lut Gölü'ne dökülüyor. Göle dökülünce oradaki sular tatlı suya dönüşecek.
9 Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
Irmağın aktığı yerlerde her çeşit canlı yaratık kaynaşacak. Çok sayıda balık olacak. Çünkü bu sular oraya akıyor, oradaki tuzlu suyu tatlı suya dönüştürüyor. Irmak aktığı her yere yaşam getirecek.
10 Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
Irmak kıyısı boyunca balıkçılar duracak; Eyn-Gedi'den Eyn-Eglayim'e dek ağ gerecek yerler olacak. Akdeniz'deki gibi çok sayıda balık çeşidi olacak.
11 Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
Ama Lut Gölü'nün çamurlu, bataklık kesimi tatlı suya dönüşmeyecek, tuzla olarak kalacak.
12 ’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
Irmağın her iki yanında her çeşit meyve ağacı yetişecek. Yaprakları solmayacak, meyveleri tükenmeyecek. Her ay meyve verecekler, çünkü tapınaktan çıkan sular oraya akıyor. Meyveleri yiyecek olarak, yaprakları şifa için kullanılacak.”
13 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
Egemen RAB şöyle diyor: “Ülkeyi mülk olarak İsrail'in on iki oymağına böleceğiniz sınırlar şöyle olacak: Yusuf'a iki pay düşecek.
14 Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
Ülkeyi on iki oymak arasında eşit olarak paylaşacaksınız. Ülkeyi atalarınıza vereceğime ant içtim. Bu ülke size mülk olarak verilecek.
15 “Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
“Ülkenin sınırı şöyle olacak: Kuzeyde Akdeniz'den, Hetlon yoluyla Levo-Hamat'a, Sedat'a,
16 Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
Berota'ya ve Şam'la Hama'nın toprakları arasında bulunan Sivrayim'e, Havran sınırında Haser-Hattikon'a kadar uzanacak.
17 Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
Sınır denizden Hasar-Enan'a, Şam'ın kuzey sınırı boyunca uzanacak, Hama sınırı kuzeyde olacak. Kuzey sınırı bu olacak.
18 A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
“Doğuda sınır Havran'la Şam arasında Gilat'ı İsrail'den ayıran Şeria Irmağı boyunca Lut Gölü'ne ve Tamar'a dek uzanacak. Doğu sınırı bu olacak.
19 A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
“Güneyde sınır Tamar'dan Meriva-Kadeş sularına, Mısır Vadisi boyunca Akdeniz'e dek uzanacak. Güney sınırı bu olacak.
20 A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
“Batıda Levo-Hamat'ın karşısındaki noktaya dek Akdeniz sınır oluşturacak. Batı sınırı bu olacak.
21 “Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
“Bu ülkeyi İsrail oymaklarına göre aranızda paylaşacaksınız.
22 Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
Ülkeyi içinizde yaşayan ve içinizdeyken çocukları olan yabancılarla kendiniz arasında mülk olarak bölüşeceksiniz. Onları İsrail'de doğan yerliler sayacaksınız. Onların da İsrail oymakları arasında sizin gibi mülkleri olacak.
23 A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Yabancı hangi oymağa yerleşmişse, orada ona düşen payı mülk olarak vereceksiniz.” Egemen RAB böyle diyor.

< Ezekiyel 47 >