< Ezekiyel 47 >

1 Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
Then the man took me back to the entrance to the temple, and there was water flowing out from under the temple threshold of the house toward the east—for the front of the temple faced east—and the water was flowing down the south side of the temple, to the right of the altar.
2 Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
So he brought me out through the northern gate and led around to the gate facing east, and there the water was flowing from this gate on its south side.
3 Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
As the man was going toward the east, there was a measuring line in his hand; he measured off one thousand cubits and brought me through the water to ankle-deep water.
4 Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
Then he measured one thousand cubits again and brought me through the water to knee-deep water; and he measured another thousand cubits and brought me to hip-deep water.
5 Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
Next he measured off another thousand cubits, but it was a river that I could not cross through because the water had risen and was deep enough to swim in—it was a river that could not be crossed.
6 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
The man said to me, “Son of man, do you see this?” and he brought me out and had me walk back along the riverbank.
7 Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
As I walked back, there the riverbank had many trees on this side and also the other side.
8 Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
The man said to me, “This water is going out to the eastern territory and down to the Arabah; this water flows into the Salt Sea and will make it fresh.
9 Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
It will be that every living creature that swarms will live where the water goes; there will be many fish, for these waters flow there. It will make the salt water fresh. Everything will live wherever the river goes.
10 Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
Then it will happen that fishermen of En Gedi will stand by the water, and there will be a place to dry out the fishing nets by En Eglaim. There will be many kinds of fish in the Salt Sea, like the fish in the Great Sea for their abundance.
11 Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
But the Salt Sea's swamps and marshes will not be made fresh; they will be for providing salt.
12 ’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
Beside this river on its banks, on both sides, all kinds of trees will grow that bear food. Their leaves will not wither and their fruit will never fail to grow. Each month the trees will bear fruit, because the water from the sanctuary flows to them. Their fruit will be for food, and their leaves will be for healing.
13 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
The Lord Yahweh says this: This will be the way that you divide the land up for the twelve tribes of Israel: Joseph will have two portions.
14 Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
You are to divide equally what I lifted up my hand and swore to give to your fathers. This land will come to you as an inheritance.
15 “Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
This will be the boundary of the land on the north side from the Great Sea by way of Hethlon, and then to Zedad.
16 Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
Then the boundary will go to Berothah, to Sibraim, which is between Damascus and Hamath, and then to Hazer Hattikon, which is beside the boundary of Hauran.
17 Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
So the boundary will go from the sea to Hazar Enan on the border with Damascus and Hamath to the north. This will be the north side.
18 A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
On the east side the boundary will run between Hauran and Damascus, along the Jordan River between Gilead and the land of Israel. You will measure from the border to the eastern sea. This will be the eastern border.
19 A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
Then on the south side the boundary will run from Tamar as far as the waters of Meribah Kadesh, then along the brook of Egypt to the Great Sea. This will be the boundary on the south side.
20 A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
Then the boundary on the west side will be the Great Sea to a point opposite Lebo Hamath. This will be the west side.
21 “Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
In this way you will divide this land for yourselves, for the tribes of Israel.
22 Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
So you will distribute the inheritances for yourselves and for the foreigners in your midst, those who have given birth to children in your midst and who are, with you, like the native born people of Israel. You will cast lots for inheritances among the tribes of Israel.
23 A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Then it will happen that the foreigner will be with the tribe among whom he is living. You must give him an inheritance—this is the Lord Yahweh's declaration.”

< Ezekiyel 47 >