< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
Und du, Menschensohn, weissage wider Gog und sprich: So spricht der Herr Jehovah: Siehe, Ich bin wider dich, Gog, Fürst, Haupt über Meschech und Thubal.
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
Und Ich wende dich zurück und sechsteile dich und lasse dich von den Seiten der Mitternacht heraufsteigen und bringe dich herein auf die Berge Israels.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
Und schlage dir deinen Bogen aus deiner linken Hand und lasse dir deine Pfeile aus der rechten Hand fallen.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
Auf den Bergen Israels sollst du fallen, du und alle deine Scharen, und die Völker, die mit dir sind; und den Raubvögeln, den Vögeln jeglichen Flügels und dem wilden Tier des Feldes gebe Ich dich zur Speise.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Auf dem Angesichte des Feldes sollst du fallen, denn Ich habe geredet, spricht der Herr Jehovah.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
Und Feuer sende Ich gegen Magog und die, so sicher auf den Inseln wohnen, auf daß sie erkennen, daß Ich Jehovah bin.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
Und den Namen Meiner Heiligkeit tue Ich kund inmitten Meines Volkes Israel, und lasse nicht mehr entweihen den Namen Meiner Heiligkeit, und erkennen sollen die Völkerschaften, daß Ich Jehovah bin, der Heilige in Israel.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
Siehe, es kommt und es geschieht, spricht der Herr Jehovah, dies ist der Tag, von dem Ich geredet habe.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
Und die, so in den Städten Israels wohnen, gehen hinaus und brennen, und feuern mit Waffen, und mit Tartsche und Schild, mit dem Bogen und Pfeilen und dem Stecken der Hand, und mit dem Speere; und Feuer davon brennen sie sieben Jahre.
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Und sie werden kein Holz vom Feld tragen, noch es hauen aus den Wäldern; denn mit den Waffen lassen sie brennen das Feuer. Und sie machen Beute von denen, welchen sie zur Beute waren, und rauben von ihren Räubern, spricht der Herr Jehovah.
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
Und am selbigen Tage wird geschehen, daß Ich dem Gog dort Platz für ein Grab in Israel gebe, die Schlucht der Vorübergehenden, ostwärts vom Meere, und es ist eine Sperre für die Vorübergehenden; und dort werden sie den Gog und all seine Volksmenge begraben und es nennen die Schlucht der Volksmenge Gogs.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
Und das Haus Israel wird sie begraben, um das Land zu reinigen, sieben Monate.
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Und alles Volk des Landes wird begraben, und es wird ihnen zum Namen sein an dem Tag, da Ich Mich verherrliche, spricht der Herr Jehovah.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
Und beständige Männer werden sie ausscheiden, die das Land durchziehen und mit den Durchziehenden begraben sie die, so auf den Angesichten des Landes übriggeblieben sind, es zu reinigen. Nach dem Ende von sieben Monaten werden sie forschen.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
Und die Durchziehenden werden das Land durchziehen, und sieht einer das Gebein eines Menschen, so baut er ein Mahlzeichen daneben auf, bis die Begrabenden es in Ge-Hamon-Gog begraben.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
Und auch der Name der Stadt ist Hamonah, und sie reinigen das Land.
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
Und du, Menschensohn, so spricht der Herr Jehovah: Sprich zu den Vögeln jeglichen Flügels und zu allem wilden Tiere des Feldes: Tut euch zusammen und kommet, versammelt euch ringsumher zu Meinem Opfer, das Ich für euch opfere, ein großes Opfer auf den Bergen Israels, und esset Fleisch und trinket Blut.
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
Das Fleisch der Helden sollt ihr essen, und das Blut der Fürsten der Erde trinken, Widder, Lämmer und Böcke, Farren, die gemästeten Baschans allzumal.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
Und ihr sollt Fett essen bis zur Sättigung, und Blut trinken bis zur Trunkenheit von Meinem Opfer, das Ich für euch opfere.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Und sättigt euch an Meinem Tisch von Roß und Streitwagen, vom Helden und jeglichem Manne des Streites, spricht der Herr Jehovah.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
Und Ich werde Meine Herrlichkeit unter die Völkerschaften geben, daß alle Völkerschaften sehen Mein Gericht, das Ich habe geübt, und Meine Hand, die Ich an sie gelegt.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
Und daß sie, das Haus Israel, wissen, daß Ich, Jehovah, ihr Gott bin von diesem Tage an und hinfort.
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
Und daß wissen die Völkerschaften, daß die vom Hause Israel ob ihrer Missetat fortgeführt wurden, weil sie Mir untreu wurden; darum Ich Mein Angesicht verbarg vor ihnen und sie in die Hände ihrer Dränger gab, so daß sie allesamt durch das Schwert fielen.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
Ob ihrer Unreinheiten und ihrer Übertretungen habe Ich so getan an ihnen und Mein Angesicht verborgen vor denselben.
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
Darum spricht so der Herr Jehovah: Nun bringe Ich die Gefangenschaft Jakobs zurück und erbarme Mich des ganzen Hauses Israel und eifere für den Namen Meiner Heiligkeit.
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
Und sie sollen tragen ihre Schande und alle ihre Untreue, die sie begingen gegen Mich, wenn sie in Sicherheit auf ihrem Boden wohnen und niemand sie aufscheucht.
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
Wenn Ich sie aus den Völkern zurückbringe und sie zusammenbringe aus den Ländern ihrer Feinde, und Mich heilige an ihnen vor den Augen vieler Völkerschaften;
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
Und sie sollen wissen, daß Ich Jehovah bin, ihr Gott, Der sie wegführte unter die Völkerschaften, und sie wieder zusammenfaßte auf ihren Boden und keinen mehr von ihnen übrig ließ;
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Und will Mein Angesicht nicht mehr verbergen vor ihnen, weil Meinen Geist Ich über das Haus Israel ausgießen werde, spricht der Herr Jehovah.

< Ezekiyel 39 >