< Ezekiyel 38 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Éternel me fut adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
Fils de l'homme, tourne ta face vers Gog, au pays de Magog, vers le prince de Rosh, de Méshec et de Tubal, et prophétise contre lui;
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
Et dis: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Voici, j'en veux à toi, Gog, prince de Rosh, de Méshec et de Tubal;
4 Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
Je t'entraînerai, et je mettrai une boucle à tes mâchoires, et je te ferai sortir avec toute ton armée, avec les chevaux et les cavaliers, tous parfaitement équipés, grande multitude armée d'écus et de boucliers, et tous maniant l'épée.
5 Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
Ceux de Perse, d'Éthiopie, de Put, sont avec eux, portant tous des boucliers et des casques;
6 haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
Gomer et toutes ses troupes, la maison de Togarma à l'extrême nord, avec toutes ses troupes, peuples nombreux qui t'accompagnent.
7 “‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
Sois prêt, prépare-toi, toi et toute la multitude assemblée avec toi; sois leur chef.
8 Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
Après beaucoup de jours, tu seras sommé; dans la suite des années tu viendras en un pays délivré de l'épée et rassemblé d'entre plusieurs peuples, sur les montagnes d'Israël, longtemps désertes; maintenant tous ramenés d'entre les nations, ils y habitent en sécurité.
9 Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
Tu t'avanceras, et tu viendras comme l'ouragan; comme une nuée tu couvriras le pays, toi, toutes tes troupes et les nombreux peuples qui sont avec toi.
10 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: En ces jours-là, des pensées monteront dans ton cœur, et tu formeras de mauvais desseins.
11 Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
Tu diras: Je monterai contre ce pays de villes sans murailles; je fondrai sur des hommes tranquilles, en sécurité dans leurs demeures, habitant tous des villes sans murailles, sans barres, ni portes.
12 Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
J'irai faire du butin et du pillage, mettre la main sur les lieux déserts qui ont été repeuplés, et sur le peuple ramené du milieu des nations, et qui soigne le bétail et ses biens, et habite au centre de la terre.
13 Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
Shéba et Dédan, les marchands de Tarsis et tous ses lionceaux, te diront: Ne viens-tu pas pour enlever du butin, et n'as-tu pas assemblé ta multitude pour faire du pillage, pour emporter de l'argent et de l'or, pour prendre le bétail et les biens, pour enlever un grand butin?
14 “Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
C'est pourquoi, fils de l'homme, prophétise, et dis à Gog: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Ne sauras-tu pas en ce jour-là qu'Israël, mon peuple, habite en sécurité?
15 Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
Et pourtant tu viendras de ton pays, de l'extrême nord, toi et plusieurs peuples avec toi, tous gens de cheval, une grande multitude et une puissante armée.
16 Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
Tu monteras contre mon peuple d'Israël, pareil à une nuée qui couvre le pays. Ce sera dans les derniers jours; je te ferai marcher contre mon pays, afin que les nations me connaissent, quand je serai sanctifié par toi sous leurs yeux, ô Gog!
17 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: N'est-ce pas de toi que j'ai parlé jadis, par le ministère de mes serviteurs les prophètes d'Israël, qui ont prophétisé alors pendant des années que je te ferai venir contre eux?
18 Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Mais, en ce jour-là, au jour où Gog marchera contre le pays d'Israël, dit le Seigneur, l'Éternel, la colère me montera au visage.
19 Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
Je le dis dans ma jalousie, dans l'ardeur de ma colère: oui, en ce jour-là, il y aura un grand trouble dans le pays d'Israël.
20 Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
Les poissons de la mer, les oiseaux des cieux, les bêtes des champs et tout reptile qui rampe sur la terre, et tous les hommes qui sont sur la face de la terre, trembleront devant moi; les montagnes seront renversées, les rochers escarpés tomberont, et toutes les murailles s'écrouleront par terre.
21 Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
Et j'appellerai contre lui l'épée sur toutes mes montagnes, dit le Seigneur, l'Éternel; l'épée de chacun se tournera contre son frère.
22 Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
Et j'entrerai en jugement avec lui par la peste et par le sang; je ferai pleuvoir sur lui, sur ses troupes, et sur les grands peuples qui l'accompagnent, une pluie violente, des grêlons, du feu et du soufre.
23 Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’
Et je me glorifierai, et je me sanctifierai, et je me ferai connaître aux yeux de nations nombreuses, et elles sauront que je suis l'Éternel.

< Ezekiyel 38 >