< Ezekiyel 12 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
The word of the LORD also came unto me, saying:
2 ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
'Son of man, thou dwellest in the midst of the rebellious house, that have eyes to see, and see not, that have ears to hear, and hear not; for they are a rebellious house.
3 “Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
Therefore, thou son of man, prepare thee stuff for exile, and remove as though for exile by day in their sight; and thou shalt remove from thy place to another place in their sight; it may be they will perceive, for they are a rebellious house.
4 Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
And thou shalt bring forth thy stuff by day in their sight, as stuff for exile; and thou shalt go forth thyself at even in their sight, as when men go forth into exile.
5 Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
Dig thou through the wall in their sight, and carry out thereby.
6 Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
In their sight shalt thou bear it upon thy shoulder, and carry it forth in the darkness; thou shalt cover thy face, that thou see not the ground; for I have set thee for a sign unto the house of Israel.'
7 Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
And I did so as I was commanded: I brought forth my stuff by day, as stuff for exile, and in the even I digged through the wall with my hand; I carried out in the darkness, and bore it upon my shoulder in their sight.
8 Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And in the morning came the word of the LORD unto me, saying:
9 “Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
'Son of man, hath not the house of Israel, the rebellious house, said unto thee: What doest thou?
10 “Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
Say thou unto them: Thus saith the Lord GOD: Concerning the prince, even this burden, in Jerusalem, and all the house of Israel among whom they are,
11 Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
say: I am your sign: like as I have done, so shall it be done unto them — they shall go into exile, into captivity.
12 “Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
And the prince that is among them shall bear upon his shoulder, and go forth in the darkness; they shall dig through the wall to carry out thereby; he shall cover his face, that he see not the ground with his eyes.
13 Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
My net also will I spread upon him, and he shall be taken in My snare; and I will bring him to Babylon to the land of the Chaldeans; yet shall he not see it, though he shall die there.
14 Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
And I will disperse toward every wind all that are round about him to help him, and all his troops; and I will draw out the sword after them.
15 “Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
And they shall know that I am the LORD, when I shall scatter them among the nations, and disperse them in the countries.
16 Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
But I will leave a few men of them from the sword, from the famine, and from the pestilence; that they may declare all their abominations among the nations whither they come; and they shall know that I am the LORD.'
17 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Moreover the word of the LORD came to me, saying:
18 “Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
'Son of man, eat thy bread with quaking, and drink thy water with trembling and with anxiety;
19 Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
and say unto the people of the land: Thus saith the Lord GOD concerning the inhabitants of Jerusalem in the land of Israel. They shall eat their bread with anxiety, and drink their water with appalment, that her land may be desolate from all that is therein, because of the violence of all them that dwell therein.
20 Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
And the cities that are inhabited shall be laid waste, and the land shall be desolate; and ye shall know that I am the LORD.'
21 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the LORD came unto me, saying:
22 “Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
'Son of man, what is that proverb that ye have in the land of Israel, saying: The days are prolonged, and every vision faileth?
23 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
Tell them therefore: Thus saith the Lord GOD: I will make this proverb to cease, and they shall no more use it as a proverb in Israel; but say unto them: The days are at hand, and the word of every vision.
24 Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
For there shall be no more any vain vision nor smooth divination within the house of Israel.
25 Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
For I am the LORD; I will speak, what word soever it be that I shall speak, and it shall be performed; it shall be no more delayed; for in your days, O rebellious house, will I speak the word, and will perform it, saith the Lord GOD.'
26 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Again the word of the LORD came to me, saying:
27 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
'Son of man, behold, they of the house of Israel say: The vision that he seeth is for many days to come, and he prophesieth of times that are far off.
28 “Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Therefore say unto them: Thus saith the Lord GOD: There shall none of My words be delayed any more, but the word which I shall speak shall be performed, saith the Lord GOD.'

< Ezekiyel 12 >