< Fitowa 19 >

1 A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
In the third month after the children of Israel [God prevails] had gone out of the land of Egypt [Abode of slavery], on that same day they came into the wilderness of Sinai [Thorn].
2 Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
When they had departed from Rephidim, and had come to the wilderness of Sinai [Thorn], they encamped in the wilderness; and there Israel [God prevails] encamped before the mountain.
3 Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
Moses [Drawn out] went up to God, and Adonai called to him out of the mountain, saying, “This is what you shall tell the house of Jacob [Supplanter], and tell the children of Israel [God prevails]:
4 ‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
‘You have seen what I did to the Egyptians [people from Abode of slavery], and how I bore you on eagles’ wings, and brought you to myself.
5 Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
Now therefore, if you will indeed sh'ma ·hear obey· my voice, and sh'ma ·hear obey· keep my covenant ·binding contract between two or more parties·, then you shall be my own segulah ·special treasure· from among all peoples; for all the earth is mine;
6 za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
and you shall be to me a kingdom of priests, and a holy nation.’ These are the words which you shall speak to the children of Israel [God prevails].”
7 Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
Moses [Drawn out] came and called for the elders of the people, and set before them all these words which Adonai enjoined him.
8 Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
All the people answered together, and said, “All that Adonai has spoken we will do.” Moses [Drawn out] reported the words of the people to Adonai.
9 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
Adonai said to Moses [Drawn out], “Behold, I come to you in a thick cloud, that the people may sh'ma ·hear obey· when I speak with you, and may also believe you forever.” Moses [Drawn out] told the words of the people to Adonai.
10 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
Adonai said to Moses [Drawn out], “Go to the people, and sanctify them today and tomorrow, and let them wash their garments,
11 Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
and be ready against the third day; for on the third day Adonai will come down in the sight of all the people on Mount Sinai [Thorn].
12 Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
You shall set bounds to the people all around, saying, ‘Be careful that you don’t go up onto the mountain, or touch its border. Whoever touches the mountain shall be surely put to death.
13 Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
No hand shall touch him, but he shall surely be stoned or shot through; whether it is animal or man, he shall not live.’ When the trumpet sounds long, they shall come up to the mountain.”
14 Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
Moses [Drawn out] went down from the mountain to the people, and sanctified the people; and they washed their clothes.
15 Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
He said to the people, “Be ready by the third day. Don’t have sexual relations with a woman.”
16 A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
On the third day, when it was morning, there were thunders and lightnings, and a thick cloud on the mountain, and the sound of an exceedingly loud shofar ·ram horn·; and all the people who were in the camp trembled.
17 Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
Moses [Drawn out] led the people out of the camp to meet God; and they stood at the lower part of the mountain.
18 Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
All of Mount Sinai [Thorn] smoked, because Adonai descended on it in fire; and its smoke ascended like the smoke of a furnace, and the whole mountain quaked greatly.
19 sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
When the sound of the shofar ·ram horn· grew louder and louder, Moses [Drawn out] spoke, and God answered him by a voice.
20 Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
Adonai came down on Mount Sinai [Thorn], to the top of the mountain. Adonai called Moses [Drawn out] to the top of the mountain, and Moses [Drawn out] went up.
21 sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
Adonai said to Moses [Drawn out], “Go down, warn the people, lest they break through to Adonai to gaze, and many of them perish.
22 Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
Let the priests also, who come near to Adonai, sanctify themselves, lest Adonai break out on them.”
23 Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
Moses [Drawn out] said to Adonai, “The people can’t come up to Mount Sinai [Thorn], for you warned us, saying, ‘Set bounds around the mountain, and sanctify it.’”
24 Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
Adonai said to him, “Go down! You shall bring Aaron [Light-bringer] up with you, but don’t let the priests and the people break through to come up to Adonai, lest he break out against them.”
25 Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.
So Moses [Drawn out] went down to the people, and told them.

< Fitowa 19 >