< Fitowa 1 >

1 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
Or, voici les noms des fils d'Israël qui vinrent en Égypte avec Jacob. Ils y vinrent chacun avec sa famille.
2 Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
Ruben, Siméon, Lévi et Juda,
3 Issakar, Zebulun da Benyamin;
Issacar, Zabulon et Benjamin,
4 Dan da Naftali; Gad da Asher.
Dan et Nephtali, Gad et Asser.
5 Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
Toutes les personnes issues de Jacob étaient soixante et dix; et Joseph était en Égypte.
6 Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
Or Joseph mourut, ainsi que tous ses frères, et toute cette génération.
7 amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
Et les enfants d'Israël s'accrurent et foisonnèrent, et se multiplièrent et devinrent très puissants; et le pays en fut rempli.
8 Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
Mais il s'éleva sur l'Égypte un nouveau roi, qui n'avait point connu Joseph.
9 Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
Et il dit à son peuple: Voici, le peuple des enfants d'Israël est plus grand et plus puissant que nous;
10 Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
Allons! agissons prudemment avec lui, de peur qu'il ne s'accroisse, et que s'il arrive quelque guerre, il ne se joigne aussi à nos ennemis, ne combatte contre nous, et ne monte hors du pays.
11 Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
Ils établirent donc sur lui des chefs de corvées, pour l'accabler par leurs travaux; et il bâtit pour Pharaon des villes de munitions, Pithom et Ramsès.
12 Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
Mais plus ils l'accablaient, plus il multipliait et se répandait; et ils prirent peur des enfants d'Israël.
13 ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
Et les Égyptiens firent servir les enfants d'Israël avec rigueur;
14 Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
Et ils leur rendirent la vie amère, par un rude travail à l'argile et aux briques, et par toutes sortes de travaux des champs, ainsi que tous les services qu'ils leur imposaient avec rigueur.
15 Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
Le roi d'Égypte parla aussi aux sages-femmes des Hébreux, dont l'une s'appelait Shiphra, et l'autre Pua,
16 “Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
Et il dit: Quand vous accoucherez les femmes des Hébreux, et que vous les verrez sur les sièges, si c'est un fils, vous le ferez mourir; mais si c'est une fille, qu'elle vive.
17 Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
Mais les sages-femmes craignirent Dieu, et ne firent pas ce que le roi d'Égypte leur avait dit; et elles laissèrent vivre les garçons.
18 Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
Alors le roi d'Égypte appela les sages-femmes, et leur dit: Pourquoi avez-vous fait ainsi, et avez-vous laissé vivre les garçons?
19 Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
Et les sages-femmes répondirent à Pharaon: C'est que les femmes des Hébreux ne sont point comme les Égyptiennes, car elles sont vigoureuses; avant que la sage-femme arrive auprès d'elles, elles ont accouché.
20 Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
Et Dieu fit du bien aux sages-femmes; et le peuple se multiplia et devint très nombreux.
21 Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
Et parce que les sages-femmes craignirent Dieu, il fit prospérer leurs maisons.
22 Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”
Alors Pharaon donna cet ordre à tout son peuple: Jetez dans le fleuve tous les fils qui naîtront, mais laissez vivre toutes les filles.

< Fitowa 1 >