< Mai Hadishi 3 >

1 Akwai lokaci domin kowane abu, da kuma lokaci domin kowane aiki a duniya.
To every [thing there is] a season, and a time to every purpose under the heaven:
2 Lokacin haihuwa da lokacin mutuwa, lokacin shuki da lokacin tumɓukewa.
A time to be born, and a time to die; a time to plant, and a time to pluck up [that which is] planted;
3 Lokacin kisa da lokacin warkarwa, lokacin rushewa da lokacin ginawa.
A time to kill, and a time to heal; a time to break down, and a time to build up;
4 Lokacin kuka da lokacin dariya, lokacin makoki da lokacin rawa.
A time to weep, and a time to laugh; a time to mourn, and a time to dance;
5 Lokacin warwatsa duwatsu da lokacin tara su, lokacin runguma da lokacin dainawa.
A time to cast away stones, and a time to gather stones together; a time to embrace, and a time to refrain from embracing;
6 Lokacin nema, da lokacin fid da zuciya, lokacin ajiyewa da lokacin zubarwa.
A time to get, and a time to lose; a time to keep, and a time to cast away;
7 Lokacin yagewa da lokacin ɗinkewa, lokacin yin shiru da lokacin magana.
A time to rend, and a time to sew; a time to keep silence, and a time to speak;
8 Lokacin ƙauna da lokacin ƙiyayya, lokacin yaƙi da lokacin salama.
A time to love, and a time to hate; a time of war, and a time of peace.
9 Wace riba ce ma’aikaci yake da ita saboda wahalarsa?
What profit hath he that worketh in that wherein he laboureth?
10 Na ga nawayar da Allah ya ɗora a kan mutane.
I have seen the travail, which God hath given to the sons of men to be exercised in it.
11 Ya yi kowane abu da kyau a lokacinsa. Ya kuma sa matuƙa a zukatan mutane, duk da haka sun kāsa gane abin da Allah ya yi daga farko zuwa ƙarshe.
He hath made every [thing] beautiful in his time: also he hath set the world in their heart, so that no man can find out the work that God maketh from the beginning to the end.
12 Na san ba abin da ya fi wa mutane kyau fiye da su ji daɗi su kuma yi alheri yayinda suke da rai.
I know that [there is] no good in them, but for [a man] to rejoice, and to do good in his life.
13 Cewa kowa yă ci, yă sha, yă kuma ji daɗi cikin dukan aikinsa, wannan kyautar Allah ce.
And also that every man should eat and drink, and enjoy the good of all his labour, it [is] the gift of God.
14 Na san cewa duk abin da Allah ya yi zai dawwama har abada; ba abin da za a ƙara ko a rage. Allah ya yi haka domin mutane su girmama shi.
I know that, whatsoever God doeth, it shall be for ever: nothing can be put to it, nor any thing taken from it: and God doeth [it], that [men] should fear before him.
15 Duk abin da yana nan ya taɓa kasancewa, kuma abin da zai kasance, ya taɓa kasancewa; Allah kuma zai nemi bayanin abubuwan da suka wuce.
That which hath been is now; and that which is to be hath already been; and God requireth that which is past.
16 Sai na ga wani abu kuma a duniya, a wurin shari’a, akwai mugunta a can, a wurin adalci, akwai mugunta a can.
And moreover I saw under the sun the place of judgment, [that] wickedness [was] there; and the place of righteousness, [that] iniquity [was] there.
17 Sai na yi tunani a zuciyata, “Allah zai shari’anta masu adalci da masu mugunta, gama za a kasance da lokaci domin kowane aiki, lokaci domin kowane abu.”
I said in mine heart, God shall judge the righteous and the wicked: for [there is] a time there for every purpose and for every work.
18 Na sāke yin tunani, “Game da mutane kam, Allah kan gwada su don su san cewa ba su fi dabba ba.
I said in mine heart concerning the estate of the sons of men, that God might manifest them, and that they might see that they themselves are beasts.
19 Ƙaddarar mutum ɗaya take da ta dabba; ƙaddara ɗaya ce take jiransu biyu. Yadda ɗayan yake mutuwa, haka ma ɗayan. Dukansu numfashinsu iri ɗaya ne; mutum bai fi dabba ba. Kowane abu ba shi da amfani.
For that which befalleth the sons of men befalleth beasts; even one thing befalleth them: as the one dieth, so dieth the other; yea, they have all one breath; so that a man hath no preeminence above a beast: for all [is] vanity.
20 Duka wuri ɗaya za su tafi; gama duka daga turɓaya suka fito, kuma ga turɓaya duka za su koma.
All go unto one place; all are of the dust, and all turn to dust again.
21 Wa ya tabbatar cewa ruhun mutum yakan tashi sama sa’an nan na dabba yă sauka ƙasa?”
Who knoweth the spirit of man that goeth upward, and the spirit of the beast that goeth downward to the earth?
22 Saboda haka na ga babu abin da ya fi kyau wa mutum fiye da yă more wahalar aikinsa, domin wannan ne rabonsa. Gama wa zai kawo shi yă ga abin da zai faru a bayansa?
Wherefore I perceive that [there is] nothing better, than that a man should rejoice in his own works; for that [is] his portion: for who shall bring him to see what shall be after him?

< Mai Hadishi 3 >