< Maimaitawar Shari’a 34 >

1 Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
Moses went up from the plains of Moab to Mount Nebo, to the top of Pisgah, that is opposite Jericho. Yahweh showed him all the land of Gilead to Dan,
2 da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
and all Naphtali, and the land of Ephraim and Manasseh, and all the land of Judah, to the Western Sea,
3 da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
and the south, and the Plain of the valley of Jericho the city of palm trees, to Zoar.
4 Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
Yahweh said to him, “This is the land which I swore to Abraham, to Isaac, and to Jacob, saying, ‘I will give it to your offspring.’ I have caused you to see it with your eyes, but you shall not go over there.”
5 Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
So Moses the servant of Yahweh died there in the land of Moab, according to Yahweh’s word.
6 Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
He buried him in the valley in the land of Moab opposite Beth Peor, but no man knows where his tomb is to this day.
7 Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
Moses was one hundred twenty years old when he died. His eye was not dim, nor his strength gone.
8 Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
The children of Israel wept for Moses in the plains of Moab thirty days, until the days of weeping in the mourning for Moses were ended.
9 To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
Joshua the son of Nun was full of the spirit of wisdom, for Moses had laid his hands on him. The children of Israel listened to him, and did as Yahweh commanded Moses.
10 Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
Since then, there has not arisen a prophet in Israel like Moses, whom Yahweh knew face to face,
11 wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
in all the signs and the wonders which Yahweh sent him to do in the land of Egypt, to Pharaoh, and to all his servants, and to all his land,
12 Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.
and in all the mighty hand, and in all the awesome deeds, which Moses did in the sight of all Israel.

< Maimaitawar Shari’a 34 >