< Maimaitawar Shari’a 32 >

1 Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
Attend, O heaven, and I will speak; and let the earth hear the words out of my mouth.
2 Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
Let my speech be looked for as the rain, and my words come down as dew, as the shower upon the herbage, and as snow upon the grass.
3 Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
For I have called on the name of the Lord: assign you greatness to our God.
4 Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
[As for God], his works [are] true, and all his ways [are] judgement: God [is] faithful, and there is no unrighteousness [in him]; just and holy [is] the Lord.
5 Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
They have sinned, not [pleasing] him; spotted children, a froward and perverse generation.
6 Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
Do you thus recompense the Lord? [is the] people thus foolish and unwise? did not he himself your father purchase you, and make you, and form you?
7 Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
Remember the days of old, consider the years for past ages: ask your father, and he shall relate to you, your elders, and they shall tell you.
8 Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
When the Most High divided the nations, when he separated the sons of Adam, he set the bounds of the nations according to the number of the angels of God.
9 Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
And his people Jacob became the portion of the Lord, Israel was the line of his inheritance.
10 A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
He maintained him in the wilderness, in burning thirst and a dry land: he led him about and instructed him, and kept him as the apple of an eye.
11 kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
As an eagle would watch over his brood, and yearns over his young, receives them having spread his wings, and takes them up on his back:
12 Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
the Lord alone led them, there was no strange god with them.
13 Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
He brought them up on the strength of the land; he fed them with the fruits of the fields; they sucked honey out of the rock, and oil out of the solid rock.
14 da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
Butter of cows, and milk of sheep, with the fat of lambs and rams, of calves and kids, with fat of kidneys of wheat; and he drank wine, the blood of the grape.
15 Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
So Jacob ate and was filled, and the beloved one kicked; he grew fat, he became thick and broad: then he forsook the God that made him, and departed from God his Saviour.
16 Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
They provoked me to anger with strange gods; with their abominations they bitterly angered me.
17 Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
They sacrificed to devils, and not to God; to gods whom they knew not: new and fresh [gods] came in, whom their fathers knew not.
18 Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
You have forsaken God that begot you, and forgotten God who feeds you.
19 Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
And the Lord saw, and was jealous; and was provoked by the anger of his sons and daughters,
20 Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
and said, I will turn away my face from them, and will show what shall happen to them in the last days; for it is a perverse generation, sons in whom is no faith.
21 Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
They have provoked me to jealousy with [that which is] not God, they have exasperated me with their idols; and I will provoke them to jealousy with them that are no nation, I will anger them with a nation void of understanding.
22 Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol h7585)
For a fire has been kindled out of my wrath, it shall burn to hell below; it shall devour the land, and the fruits of it; it shall set on fire the foundations of the mountains. (Sheol h7585)
23 “Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
I will gather evils upon them, and will fight with my weapons against them.
24 Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
[They shall be] consumed with hunger and the devouring of birds, and there shall be irremediable destruction: I will send forth against them the teeth of wild beasts, with the rage of [serpents] creeping on the ground.
25 Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
Without, the sword shall bereave them of children, and terror [shall issue] out of the secret chambers; the young man shall perish with the virgin, the suckling with him who has grown old.
26 Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
I said, I will scatter them, and I will cause their memorial to cease from amongst men.
27 Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
Were it not for the wrath of the enemy, lest they should live long, lest their enemies should combine against them; lest they should say, Our own high arm, and not the Lord, has done all these things.
28 Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
It is a nation that has lost counsel, neither is there understanding in them.
29 A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
They had not sense to understand: let them reserve these things against the time to come.
30 Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
How should one pursue a thousand, and two rout tens of thousands, if God had not sold them, and the Lord delivered them up?
31 Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
For their gods are not as our God, but our enemies [are] void of understanding.
32 Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
For their vine [is] of the vine of Sodom, and their vine-branch of Gomorrha: their grape [is] a grape of gall, their cluster [is] one of bitterness.
33 Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
Their wine [is] the rage of serpents, and the incurable rage of asps.
34 “Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
Behold! are not these things stored up by me, and sealed amongst my treasures?
35 Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
In the day of vengeance I will recompense, whenever their foot shall be tripped up; for the day of their destruction [is] near to them, and the judgements at hand are close upon you.
36 Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
For the Lord shall judge his people, and shall be comforted over his servants; for he saw that they were utterly weakened, and failed in the hostile invasion, and were become feeble:
37 Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
and the Lord said, Where are their gods on whom they trusted?
38 allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
the fat of whose sacrifices you ate, and you drank the wine of their drink-offerings? let them arise and help you, and be your protectors.
39 “Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
Behold, behold that I am [he], and there is no god beside me: I kill, and I will make to live: I will strike, and I will heal; and there is none who shall deliver out of my hands.
40 Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
For I will lift up my hand to heaven, and swear by my right hand, and I will say, I live for ever.
41 sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
For I will sharpen my sword like lightning, and my hand shall take hold of judgement; and I will render judgement to my enemies, and will recompense them that hate me.
42 Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
I will make my weapons drunk with blood, and my sword shall devour flesh, [it shall glut itself] with the blood of the wounded, and from the captivity of the heads of [their] enemies that rule over them.
43 Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
Rejoice, you heavens, with him, and let all the angels of God worship him; rejoice you Gentiles, with his people, and let all the sons of God strengthen themselves in him; for he will avenge the blood of his sons, and he will render vengeance, and recompense justice to his enemies, and will reward them that hate him; and the Lord shall purge the land of his people.
44 Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
And Moses wrote this song in that day, and taught it to the children of Israel; and Moses went in and spoke all the words of this law in the ears of the people, he and Joshua the [son] of Naue.
45 Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
And Moses finished speaking to all Israel.
46 ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
And he said to them, Take heed with your heart to all these words, which I testify to you this day, which you shall command your sons, to observe and do all the words of this law.
47 Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
For this [is] no vain word to you; for it [is] your life, and because of this word you shall live long upon the land, into which you go over Jordan to inherit it.
48 A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses in this day, saying,
49 “Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
Go up to the mount Abarim, this mountain Nabau which is in the land of Moab over against Jericho, and behold the land of Chanaan, which I give to the sons of Israel:
50 A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
and die in the mount whither you go up, and be added to your people; as Aaron your brother died in mount Or, and was added to his people.
51 Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
Because you disobeyed my word amongst the children of Israel, at the waters of strife of Cades in the wilderness of Sin; because you sanctified me not amongst the sons of Israel.
52 Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”
You shall see the land before [you], but you shall not enter into it.

< Maimaitawar Shari’a 32 >