< Maimaitawar Shari’a 3 >

1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
Then we turned and went up the way to Bashan. Og, the king of Bashan, came and attacked us, he and all his people, to fight at Edrei.
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
Yahweh said to me, 'Do not fear him; for I have given you victory over him and have put all his people and his land under your control. You will do to him as you did to Sihon, king of the Amorites, who lived at Heshbon.'
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
So Yahweh our God also gave us victory over Og the king of Bashan, and all his people were put under our control. We struck them down until not one of his people remained.
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
We took all his cities at that time. There was not one of the sixty cities that we did not take from them—all the region of Argob, the kingdom of Og in Bashan.
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
These were all cities fortified with high walls, gates, and bars; this was besides very many unwalled villages.
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
We completely destroyed them, as we did to Sihon king of Heshbon, completely destroying every city—men and the women and the little ones.
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
But all the cattle and the spoil of the cities, we took as spoils for ourselves.
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
At that time we took the land out of the hand of the two kings of the Amorites, who were beyond the Jordan, from the Valley of the Arnon to Mount Hermon
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
(Mount Hermon the Sidonians call Sirion, and the Amorites call it Senir)
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
and all the cities of the plain, all Gilead, and all Bashan, all the way to Salekah and Edrei, cities of the kingdom of Og in Bashan.”
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
(For of the remnant of the Rephaim, only Og king of Bashan had remained. Look! His bed was a bed of iron. Was it not in Rabbah, where the descendants of Ammon live? It was nine cubits long and four cubits wide, the way people measure.)
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
“This land that we took in possession at that time—from Aroer, that is by the Valley of the Arnon, and half the hill country of Gilead, and its cities—I gave to the Reubenites and to the Gadites.
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
The rest of Gilead and all Bashan, the kingdom of Og, I gave to the half tribe of Manasseh. (All the region of Argob, and all Bashan. The same territory is called the land of Rephaim.
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
Jair, a descendant of Manasseh, took all the region of Argob to the border of the Geshurites and the Maakathites. He called the region, even Bashan, by his own name, Havvoth Jair, to this day.)
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
I gave Gilead to Machir.
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
To the Reubenites and to the Gadites I gave territory from Gilead to the Valley of the Arnon—the middle of the valley is the territory's border—and to the Jabbok River, which is the border with the descendants of Ammon.
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
Another of its borders is also the plain of the Jordan River valley, from Kinnereth to the Sea of the Arabah (that is, the Salt Sea) to the slopes of Mount Pisgah eastward.
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
I commanded you at that time, saying, 'Yahweh your God has given you this land to possess it; you, all the men of war, will pass over armed before your brothers, the people of Israel.
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
But your wives, your little ones, and your cattle (I know that you have much cattle), will stay in your cities that I have given you,
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
until Yahweh gives rest to your brothers, as he has to you, until they also possess the land that Yahweh your God is giving them beyond the Jordan; then will you return, every man of you, to your own property that I have given you.'
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
I commanded Joshua at that time, saying, 'Your eyes have seen all that Yahweh your God has done to these two kings; Yahweh will do the same to all the kingdoms where you go over.
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
You will not fear them, for Yahweh your God is the one who will fight for you.'
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
I implored Yahweh at that time, saying,
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
'O Lord Yahweh, you have begun to show your servant your greatness and your strong hand; for what god is there in heaven or in earth that can do the same works as you have done, and the same mighty acts?
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
Let me go over, I beg you, and see the good land that is beyond the Jordan, that good hill country, and also Lebanon.'
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
But Yahweh was angry with me because of you; he did not listen to me. Yahweh said to me, 'Let this be enough for you—speak no more to me about this matter:
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
go up to the top of Pisgah and lift up your eyes westward, northward, southward, and eastward; look with your eyes, for you will not go over the Jordan.
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
Instead, instruct Joshua and encourage and strengthen him, for he will go over before this people, and he will cause them to inherit the land that you will see.'
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
So we stayed in the valley opposite Beth Peor.

< Maimaitawar Shari’a 3 >