< Daniyel 6 >

1 Ya gamshi Dariyus ya naɗa muƙaddasai 120 su yi shugabanci a duk fāɗin masarautar,
It pleased Darius to appoint over the kingdom 120 provincial governors who would rule over all the kingdom.
2 ya naɗa mutum uku a bisa waɗannan muƙaddasan, Daniyel yana ɗaya daga cikin mutum ukun nan. Sai aka sa muƙaddasan nan a ƙarƙashin waɗannan uku ɗin domin kada sarki ya yi hasarar kome.
Over them there were three chief administrators, and Daniel was one of them. These chief administrators were appointed so that they might supervise the provincial governors, so that the king should suffer no loss.
3 To, Daniyel dai ya yi ficce a cikin shugabannin nan uku har da muƙaddasan ma, saboda waɗansu halaye nagari da yake da su, wanda ya sa sarki ya yi shiri ya ɗora shi a kan dukan mulkinsa.
Daniel was distinguished above the other chief administrators and the provincial governors because he had an extraordinary spirit. The king was planning to put him over the whole kingdom.
4 A kan haka, shugabannin nan uku da muƙaddasan nan suka yi ƙoƙari su sami wani laifi a kan Daniyel a yadda yake tafiyar da aikin shugabancinsa, amma ba su samu ba. Ba su same shi da wani laifin cin hanci ba, domin shi amintacce ne kuma babu wani aibi a kansa ko rashin kula.
Then the other chief administrators and the provincial governors looked for mistakes in the work Daniel did for the kingdom, but they could find no corruption or failure in his duty because he was faithful. No mistakes or negligence was found in him.
5 A ƙarshe waɗannan mutane suka ce; “Ba za mu taɓa samun wani laifin da za mu kama Daniyel da shi ba, sai dai ko abin ya shafi dokar Allahnsa.”
Then these men said, “We cannot find any reason to complain against this Daniel unless we find something against him regarding the law of his God.”
6 Saboda haka shugabannin nan suka haɗu da muƙaddasan nan suka tafi wurin sarki a ƙungiyance suka ce, “Ya Sarki Dariyus, ranka yă daɗe!
Then these administrators and governors brought a plan before the king. They said to him, “King Darius, may you live forever!
7 Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.
All the chief administrators of the kingdom, the regional governors, and the provincial governors, the advisors, and the governors have consulted together and decided that you, the king, should issue a decree and should enforce it, so that whoever makes a petition to any god or man for thirty days, except to you, king, that person must be thrown into the den of lions.
8 Yanzu, ya sarki, sai ka yi umarni ka kuma yi shi a rubuce saboda kada a canja shi, bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
Now, King, issue a decree and sign the document so that it may not be changed, as directed by the laws of the Medes and Persians, so it cannot be repealed.”
9 Sai Sarki Dariyus ya ba da umarnin a rubuce.
So king Darius signed the document making the decree into a law.
10 To, da Daniyel ya ji labarin cewa an fitar da doka, sai ya tafi gidansa a ɗakinsa na sama inda tagogin ɗakin suke duban wajen Urushalima. Sau uku yakan durƙusa yă yi addu’a yana yin godiya ga Allahnsa, kamar yadda ya saba yi.
When Daniel learned that the document had been signed into law, he went into his house (now his windows were open in his upper room toward Jerusalem), and he got down on his knees, as he did three times a day, and prayed and gave thanks before his God, as he had done before.
11 Sai waɗannan mutane suka tafi a ƙungiyance suka kuma iske Daniyel yana addu’a yana roƙon Allah yă taimake shi.
Then these men who had formed the plot together saw Daniel make requests and seek help from God.
12 Sai suka tafi wurin sarki suka yi masa magana game da dokar mulkinsa, suka ce, “Ashe, ba ka yi doka cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda aka tarar yana addu’a ga wani allah ko mutum in ba kai ba, ya sarki, za ka jefa shi a cikin ramin zakoki ba?” Sarki ya amsa ya ce, “Dokar tana nan daram bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
Then they approached the king and spoke with him about his decree: “Did you not make a decree that everyone who makes a petition to any god or human being during the next thirty days, except to you, king, must be throw into the den of lions?” The king answered, “The matter is settled, as directed by the law of the Medes and Persians; it cannot be repealed.”
13 Sai suka ce wa sarki, “Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga Yahuda, bai kula da kai ba, ya sarki, balle fa dokar da ka yi. Har yanzu yana addu’a sau uku a rana.”
Then they replied to the king, “That person Daniel, who is one of the people of the exile from Judah, pays no attention to you, king, or to the decree that you have signed. He prays to his God three times a day.”
14 Da sarki ya ji haka, sai ya damu sosai, ya ƙudura yă ceci Daniyel, ya yi ta fama har fāɗuwar rana yadda zai yi yă kuɓutar da shi.
When the king heard this, he was terribly distressed, and he applied his mind to rescue Daniel from this ruling. He labored until sunset to try to save Daniel.
15 Sai mutanen nan suka je wurin sarki a ƙungiyance suka ce masa, “Ka tuna, ya sarki; cewa bisa ga dokar Medes da Farisa, babu umarni ko dokar da sarki ya yi da za a iya sokewa.”
Then these men who had formed the plot gathered together with the king and said to him, “Know, king, that it is a law of the Medes and Persians, that no decree or statute that the king issues can be changed.”
16 Saboda haka sai sarki ya ba da umarni suka kuma kawo Daniyel suka jefa shi cikin ramin zakoki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Bari Allahn nan wanda kake bauta masa kullum, yă cece ka!”
Then the king gave an order, and they brought in Daniel, and they threw him into the lions' den. The king said to Daniel, “May your God, whom you serve continually, rescue you.”
17 Aka kawo dutsen aka rufe bakin ramin, sa’an nan sarki ya hatimce shi da zobensa da kuma zoban manyan mutanensa, don kada wani yă canja yanayin Daniyel.
A stone was brought over the entrance to the den, and the king sealed it with his own signet ring and with the signet rings of his nobles so that nothing might be changed concerning Daniel.
18 Sa’an nan sarki ya koma fadarsa ya kwana bai ci ba, kuma babu wata liyafar da aka kawo masa. Ya kuma kāsa barci.
Then the king went to his palace and he went through the night fasting. No entertainment was brought before him, and sleep fled from him.
19 Gari yana wayewa, sai sarki ya tashi ya hanzarta zuwa ramin zakoki.
Then at daybreak the king got up and he quickly went to the lions' den.
20 Da ya yi kusa da ramin zakokin, sai ya kira Daniyel da muryar mai cike da damuwa ya ce, “Daniyel bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta wa kullum, ya iya cetonka daga zakoki?”
As he came near to the den, he called out to Daniel in a sad voice, saying to Daniel, “Daniel, servant of the living God, has your God, whom you serve continually, been able to save you from the lions?”
21 Sai Daniyel ya amsa ya ce, “Ran sarki, yă daɗe!
Then said Daniel to the king, “King, live forever!
22 Allahna ya aiko da mala’ikansa, ya kuwa rufe bakunan zakoki. Ba su yi mini rauni ba, gama an same ni marar laifi ne a gabansa. Ban kuwa taɓa yin wani abu marar kyau a gabanka ba, ya sarki.”
My God has sent his messenger and has shut the lions' mouths, and they have not hurt me. For I was found blameless before him and also before you, king, and I have done you no harm.”
23 Sai sarki ya cika da murna ƙwarai, ya kuma yi umarni a ciro Daniyel daga ramin zakoki. Kuma da aka fito da Daniyel daga ramin, ba a sami wani rauni a jikinsa ba, domin ya dogara ga Allahnsa.
Then the king was very happy. He gave an order that they should take Daniel up out of the den. So Daniel was lifted up out of the den. No harm was found on him, because he had trusted in his God.
24 Sai sarki ya umarta, a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da’ya’yansu, da matansu cikin ramin zakoki. Kafin ma su kai ƙurewar ramin, sai zakoki suka hallaka su suka yayyage su, suka yi kaca-kaca da su.
The king gave an order, and they brought those men who had accused Daniel and threw them into the den of lions—they, their children, and their wives. Before they reached the floor, the lions overpowered them and broke all their bones to pieces.
25 Sa’an nan Sarki Dariyus ya rubuta wa dukan mutane, da al’ummai da kuma mutanen dukan harsunan a duk fāɗin ƙasar. “Bari yă yi nasara sosai!
Then King Darius wrote to all the peoples, nations, and languages that live in all the earth: “May peace increase for you.
26 “Na fitar da doka cewa a cikin dukan iyakar ƙasar mulkina, dole mutane su ji tsoro su kuma girmama Allah na Daniyel.
I hereby make a decree that in all the dominion of my kingdom men tremble and fear before the God of Daniel, for he is the living God and lives forever, and his kingdom shall not be destroyed; his dominion shall be to the end.
27 Yakan kuɓutar ya kuma ceci;
He makes us safe and rescues us, and he does signs and wonders in heaven and in earth; he has kept Daniel safe from the strength of the lions.”
28 Daniyel kuwa ya bunkasa a lokacin mulkin Dariyus da kuma mulkin Sairus na Farisa.
So Daniel prospered during the reign of Darius and during the reign of Cyrus the Persian.

< Daniyel 6 >