< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
Und David redete vor dem HERRN die Worte dieses Liedes zur Zeit, da ihn der HERR errettet hatte von der Hand aller seiner Feinde und von der Hand Sauls, und sprach:
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Der HERR ist mein Fels und meine Burg und mein Erretter.
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
Gott ist mein Hort, auf den ich traue, mein Schild und Horn meines Heils, mein Schutz und meine Zuflucht, mein Heiland, der du mir hilfst vor dem Frevel.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
Ich rufe an den HERRN, den Hochgelobten, so werde ich von meinen Feinden erlöst.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Es hatten mich umfangen die Schmerzen des Todes, und die Bäche des Verderbens erschreckten mich.
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
Der Hölle Bande umfingen mich, und des Todes Stricke überwältigten mich. (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
Da mir angst war, rief ich den HERRN an und schrie zu meinem Gott; da erhörte er meine Stimme von seinem Tempel, und mein Schreien kam vor ihn zu seinen Ohren.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
Die Erde bebte und ward bewegt; die Grundfesten des Himmels regten sich und bebten, da er zornig war.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Dampf ging auf von seiner Nase und verzehrend Feuer von seinem Munde, daß es davon blitzte.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
Er neigte den Himmel und fuhr herab, und Dunkel war unter seinen Füßen.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
Und er fuhr auf dem Cherub und flog daher, und er schwebte auf den Fittichen des Windes.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
Sein Gezelt um ihn her war finster und schwarze, dicke Wolken.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Von dem Glanz vor ihm brannte es mit Blitzen.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
Der HERR donnerte vom Himmel, und der Höchste ließ seinen Donner aus.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
Er schoß seine Strahlen und zerstreute sie; er ließ blitzen und erschreckte sie.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Da sah man das Bett der Wasser, und des Erdbodens Grund ward aufgedeckt von dem Schelten des HERRN, von dem Odem und Schnauben seiner Nase.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
Er streckte seine Hand aus von der Höhe und holte mich und zog mich aus den großen Wassern.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
Er errettete mich von meinen starken Feinden, von meinen Hassern, die zu mir mächtig waren,
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
die mich überwältigten zur Zeit meines Unglücks; und der HERR ward meine Zuversicht.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
Und er führte mich aus in das Weite, er riß mich heraus; denn er hatte Lust zu mir.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
Der HERR tut wohl an mir nach meiner Gerechtigkeit; er vergilt mir nach der Reinigkeit meiner Hände.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
Denn ich halte die Wege des HERRN und bin nicht gottlos wider meinen Gott.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
Denn alle seine Rechte habe ich vor Augen, und seine Gebote werfe ich nicht von mir;
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
sondern ich bin ohne Tadel vor ihm und hüte mich vor Sünden.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Darum vergilt mir der HERR nach meiner Gerechtigkeit, nach meiner Reinigkeit vor seinen Augen.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
Bei den Heiligen bist du heilig, bei den Frommen bist du fromm,
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
bei den Reinen bist du rein, und bei den Verkehrten bist du verkehrt.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
Denn du hilfst dem elenden Volk, und mit deinen Augen erniedrigst du die Hohen.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Denn du, HERR, bist meine Leuchte; der HERR macht meine Finsternis licht.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Denn mit dir kann ich Kriegsvolk zerschlagen und mit meinem Gott über die Mauer springen.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Gottes Wege sind vollkommen; des HERRN Reden sind durchläutert. Er ist ein Schild allen, die ihm vertrauen.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Denn wo ist ein Gott außer dem HERRN, und wo ist ein Hort außer unserm Gott?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
Gott stärkt mich mit Kraft und weist mir einen Weg ohne Tadel.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
Er macht meine Füße gleich den Hirschen und stellt mich auf meine Höhen.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Er lehrt meine Hände streiten und lehrt meinen Arm den ehernen Bogen spannen.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Du gibst mir den Schild deines Heils; und wenn du mich demütigst, machst du mich groß.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Du machst unter mir Raum zu gehen, daß meine Knöchel nicht wanken.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Ich will meinen Feinden nachjagen und sie vertilgen und will nicht umkehren, bis ich sie umgebracht habe.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
Ich will sie umbringen und zerschmettern; sie sollen mir nicht widerstehen und müssen unter meine Füße fallen.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Du kannst mich rüsten mit Stärke zum Streit; du kannst unter mich werfen, die sich wider mich setzen.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
Du gibst mir meine Feinde in die Flucht, daß ich verstöre, die mich hassen.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Sie sahen sich um, aber da ist kein Helfer, nach dem HERRN; aber er antwortet ihnen nicht.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Ich will sie zerstoßen wie Staub auf der Erde; wie Kot auf der Gasse will ich sie verstäuben und zerstreuen.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Du hilfst mir von dem zänkischen Volk und behütest mich, daß ich ein Haupt sei unter den Heiden; ein Volk, das ich nicht kannte, dient mir.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Den Kindern der Fremde hat's wider mich gefehlt; sie gehorchen mir mit gehorsamen Ohren.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Die Kinder der Fremde sind verschmachtet und kommen mit Zittern aus ihren Burgen.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
Der HERR lebt, und gelobt sei mein Hort; und Gott, der Hort meines Heils, werde erhoben,
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
der Gott, der mir Rache gibt und wirft die Völker unter mich.
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
Er hilft mir aus von meinen Feinden. Du erhöhst mich aus denen, die sich wider mich setzen; du hilfst mir von den Frevlern.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Darum will ich dir danken, HERR, unter den Heiden und deinem Namen lobsingen,
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
der seinem Könige großes Heil beweist und wohltut seinem Gesalbten, David und seinem Samen ewiglich.

< 2 Sama’ila 22 >