< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
David spoke to YHWH the words of this song in the day that YHWH delivered him out of the hand of all his enemies, and out of the hand of Saul:
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
and he said, "YHWH is my Rock, and my fortress, and my deliverer.
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
My God, my Rock, in him I will take refuge, my shield, and the horn of my salvation, my high tower, and my refuge, my savior; from violent people he saves me.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
I call on YHWH, who is worthy to be praised, and I am saved from my enemies.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
For the waves of death surrounded me, and the currents of ungodliness overwhelmed me.
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
The cords of Sheol were around me. The snares of death caught me. (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
In my distress I called upon YHWH, and I cried out to my God. He heard my voice out of his temple, and my cry came into his ears.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
Then the earth shook and trembled. The foundations of the mountains quaked and were shaken, because he was angry.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Smoke went up out of his nostrils. Fire out of his mouth devoured. Coals were kindled by it.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
He bowed the heavens also, and came down. Thick darkness was under his feet.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
He rode on a cherub, and flew; and he soared on the wings of the wind.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
He made darkness his hiding place, his canopy around him thick clouds dark with water.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
From the brightness before him his thick clouds passed on, with hailstones and coals of fire.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
YHWH thundered from heaven. The Most High uttered his voice.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
And he sent out arrows and scattered them, and he shot lightning bolts and routed them.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Then the channels of the sea appeared. The foundations of the world were laid bare by the rebuke of YHWH, at the blast of the breath of his nostrils.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
He sent from on high and he took me. He drew me out of many waters.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
He delivered me from my strong enemy, from those who hated me, for they were too mighty for me.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
They came on me in the day of my calamity, but YHWH was my support.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
He also brought me out into a large place. He delivered me, because he delighted in me.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
YHWH rewarded me according to my righteousness. He rewarded me according to the cleanness of my hands.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
For I have kept the ways of YHWH, and have not wickedly departed from my God.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
For all his ordinances were before me, and his statutes I did not put away from me.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
I was also perfect toward him. I kept myself from my iniquity.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Therefore YHWH has rewarded me according to my righteousness, according to the cleanness of my hands in his sight.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
With the faithful you show yourself faithful. With the innocent you show yourself innocent.
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
With the pure you show yourself pure. And with the crooked you show yourself tortuous.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
You save a humble people, but the eyes of the proud you will bring low.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
For you light my lamp. YHWH my God lights up my darkness.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
For by you, I run against a troop. By my God, I leap over a wall.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
As for God, his way is perfect. The word of YHWH is pure. He is a shield to all those who take refuge in him.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
For who is God, besides YHWH? Who is a rock, besides our God,
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
the God who girds me with strength, and makes my way blameless?
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
He makes my feet like those of a deer, and sets me on my high places.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
He teaches my hands to war, so that my arms bend a bow of bronze.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
You have also given me the shield of your salvation, and your right hand holds me up, and your help has made me great.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
You have enlarged my steps under me. My feet have not slipped.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
I pursued my enemies and overtook them, and I did not turn back until they were destroyed.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
And I consumed them, and struck them through, so that they did not rise. And they fell beneath my feet.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
For you have equipped me with strength for the battle. You have subdued under me those who rose up against me.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
You have also made my enemies turn their backs to me, that I might cut off those who hate me.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
They cry out, but there was none to save; even to YHWH, but he did not answer them.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Then I ground them as fine as the dust on the surface of a path. Like the mud in the streets, I trampled them.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
You also have delivered me from the strivings of my people. You have kept me to be the head of the nations. A people whom I have not known will serve me.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
As soon as they hear of me they obey me. Foreigners come cringing to me;
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
they are not bound in chains.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
YHWH lives. Blessed be my rock. Exalted be God, the rock of my salvation,
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
even the God who executes vengeance for me, and subdues peoples under me,
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
who brings me away from my enemies. Yes, you lift me up above those who rise up against me. You protect me from the violent man.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Therefore I will praise you, YHWH, among the nations, and will sing praises to your name.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
He gives great deliverance to his king, and shows loving kindness to his anointed, to David and to his descendants, until forever."

< 2 Sama’ila 22 >